Rahotanni daga Arewa maso gabas na cewa Boko Haram ta kashe sojojin Najeriya 3 wasu 2 kuma sun bace a wani harin kwantan Bauna da suka kaiwa sojojin.
Boko Haram din sun budewa Sojojin wuta a Barwanti dake kusa da tafkin Chadi bayan da wani Bam din da suka binnewa sojojin ya tashi.
Majiyar kamfanin dillancin labaran AFP ta bayyana cewa, kuma Boko Haram din sun kwace motar yakin sojojin 1.
“The terrorists opened fire, killing three soldiers and seizing a gun truck,” one officer told AFP.
“Two soldiers remain missing while one was seriously injured,” he added.