Wednesday, August 13
Shadow
Gwamnatin Tinubu ta dakatar da gina sabbin makarantun Jami’a na tsawon shekaru 7 inda tace akwai makarantun jami’a da malamai sun fi dalibai yawa

Gwamnatin Tinubu ta dakatar da gina sabbin makarantun Jami’a na tsawon shekaru 7 inda tace akwai makarantun jami’a da malamai sun fi dalibai yawa

Duk Labarai
Gwamnatin tarayya ta dakatar da gina sabbin makarantun jami'a na tsawon shekaru 7. Gwamnatin tace makarantun da ake dasu a yanzu wasu malamai sun fi dalibai yawa, wasu ma ba'a neman shigarsu. An dauki wannan mataki ne a zaman majalisar zartaswa na ranar Laraba wanda shugaban kasa, Bola Ahmad Tinubu ya jagoranta. Ministan Ilimi, Tunji Alausa ya tabbatar da hakan inda yace maimakon gina sabbin jami'o'in, Gwamnati zata mayar da hankali ne wajan gyara wadanda ake dasu da kuma daukar malamai kwararru.
Kalli Bidiyo: Auren da Rahama Sadau ta yi ta kyauta, Ki daure ki zauna a gidan mijinki, ki masa biyayya>>Inji Malam

Kalli Bidiyo: Auren da Rahama Sadau ta yi ta kyauta, Ki daure ki zauna a gidan mijinki, ki masa biyayya>>Inji Malam

Duk Labarai
Malam ya yabawa Rahama Sadau bisa auren da ta yi inda yace abin zai zamewa mahaifinta Alheri kuma suna fatan zata zauna tawa mijinta biyayya. Malam ya jawo hankalin cewa, sauran mata abokan sana'arta ya kamata su yi koyi da ita. A gefe guda kuma ya soki Rahama Sa'idu kan cewa ba zatawa mijinta wanke-wanke ba. https://www.tiktok.com/@mahamansanidanhajiya/video/7537786723070184709?_t=ZS-8yqZBqRRdNx&_r=1
Sheikh Nura Khalid, Digital Imam ya goyi bayan fatawar da Sheikh Ibrahim Maqari ya baiwa Gfresh kan yin Bidiyo da iyalinsa, inda yace ba’a korar me neman shiriya

Sheikh Nura Khalid, Digital Imam ya goyi bayan fatawar da Sheikh Ibrahim Maqari ya baiwa Gfresh kan yin Bidiyo da iyalinsa, inda yace ba’a korar me neman shiriya

Duk Labarai
Babban malamin Addinin Islama, Sheikh Nura Khalid ya goyi bayan fatawar da Sheikh Ibrahim Maqari ya baiwa tauraron Tiktok, Gfresh Al-amin. Sheikh Nura Khalid yace akalla dai an rabasu da wani abu daga cikin miyagun abubuwan da suke. Yace kuma idan zasu ci gaba da sauraren wa'azi zama su daina baki daya. Ya bayyana cewa, Sheikh Maqari yayi amfani da Hikima irin ta masu wa'azi wajan bayar da fatawar. https://www.tiktok.com/@hassangiwa3/video/7537869952225774904?_t=ZS-8yqXDppBQcy&_r=1 Gfresh dai ya je gaban Maqari inda ya nemi fatawa kan Bidiyon da suke yi da iyalansu. Sai Sheikh Maqari ya bashi fatawar cewa, idan zasu rika aika sakon da'awa hakan ba matsala bane.
Bidiyo Da Duminsa: Hukumar kula da Almajirai ta kasa ta karrama Rarara saboda tallafin da yake baiwa Almajirai

Bidiyo Da Duminsa: Hukumar kula da Almajirai ta kasa ta karrama Rarara saboda tallafin da yake baiwa Almajirai

Duk Labarai
Hukumar kula da almajirai ta kasa ta karrama tauraron mawaki Dauda Kahutu Rarara saboda taimakon da yake baiwa Almajirai. Shugaban hukumar yace saboda yanda Rarara ke tallafawa rayuwar Almajirai shiyasa suka ga ya dace su bashi kyautar girmamawa. https://www.tiktok.com/@mubeedabai/video/7538014470908497208?_t=ZS-8yqVAFGi9o1&_r=1
Bidiyo Da Duminsa: Yayin da ake rade-radin bashi da lafiya Shugaba Tinubu ya halarci taron majalisar zartaswa

Bidiyo Da Duminsa: Yayin da ake rade-radin bashi da lafiya Shugaba Tinubu ya halarci taron majalisar zartaswa

Duk Labarai
Shugaban kasa, Bola Ahmad Tinubu ya halarci taron majalisar zartaswa a fadarsa ranar Laraba. A taron, Shugaba Tinubu ya rantsar da sabon shugaban hukumar kula da gyaran dokoki. https://twitter.com/TheNationNews/status/1955627359089959341?t=FUtOhxqzj7DXoL6ye7uJBA&s=19 A baya dai an rika samun rahotanni masu cewa, Shugaba Tinubu bashi da lafiya har ana shirin fita dashi zuwa kasashen waje dan magani.
Ali Nuhu ya kaiwa gwamnan jihar Gombe, Inuwa Yahya Ziyara inda yace za’a gina cibiyar yin fim a jihar sannan kuma za’a fara koyawa daliban jami’ar jihar gombe yin fim

Ali Nuhu ya kaiwa gwamnan jihar Gombe, Inuwa Yahya Ziyara inda yace za’a gina cibiyar yin fim a jihar sannan kuma za’a fara koyawa daliban jami’ar jihar gombe yin fim

Duk Labarai
Tauraron fina-finan Hausa, kuma shugaban hukumar fina-finai ta kasa, Ali Nuhu ya kaiwa Gwamnan jihar Gombe, Inuwa Yahya ziyara. Ali Nuhu yace ziyarar tasa sun tattauna muhimman baututuwa sannan ya samu tarba me kyau. Ali Nuhu yace daya daga cikin abubuwan da suka tattauna sune naganar gina cibiyar yin fim a jihar Gombe. Ali Nuhu yace cibiyar zata taimaka wajan karfafa fasaha musamman ta yin fim. Sannan yace akwai shiri na koyawa daliban jami'ar jihar Gombe yin film.
Yau wata guda kenan daidai da rashin shugaba Buhari, har yanzu ina jin zafin rashinsa, ji nake kamar yau ya rasu>>Inji Tsohon Hadimin shugaban kasa, Malam Bashir Ahmad

Yau wata guda kenan daidai da rashin shugaba Buhari, har yanzu ina jin zafin rashinsa, ji nake kamar yau ya rasu>>Inji Tsohon Hadimin shugaban kasa, Malam Bashir Ahmad

Duk Labarai
Tsohon hadimin shugaban kasa, Malam Bashir Ahmad ya bayyana alhinin tsohon shugaban kasa, Marigayi Muhammadu Buhari. Ya bayyana cewa, wata guda kenan da rasuwar shugaba Buhari inda yace Buhari ya kafa tarihi da rayuwa me nagarda wadda zata dawwama ana tunawa da ita. Ya bayyana cewa har yanzu zafin rashin Buhari bai gushe a zuciyarsa na dan ji yake kamar yaune Buharin ya rasu.