Nafiu Bala wanda ya kai Su Atiku, El-Rufai, Kwankwaso, Peter Obi Kotu yace shine shugaban APC amma suna son yi masa kwace, ya aikawa kasar Amurka Takardar korafi
Nafiu Bala Gombe wanda ke ikirarin shine shugaban jam'iyyar ADC kuma ya maka su Atiku, El-Rufai, Kwankwaso, da Peter Obi a kotu yace suna son rabashi da mukaminsa ta hanyar karfa-karfa ya aikawa kasar Amurka da korafi.
Nafiu ya ce a cikin takardar a dokar jam'iyyar ADC, idan shugaba ya sauka mataimakinsa ne ke karbar shugabancin jam'iyyar, yace dan haka da tsohon shugaban jam'iyyar ya sauka, Shine halastaccen shugaba.
Saidai yace su Atiku, El-Rufai, Kwankwaso, da Peter Obi sun je sun masa karfa-karfa.
Yace suna zargin wai shugaban kasa ne ko jam'iyyar shugaban kasa ce ta dauki nauyinsa amma yace ba gaskiya bane bashi da alaka da APC ko shugaban kasa.
Yace dan haka yana kira ga kasar Amurka data hana wadannan mutane shiga kasarta.








