Sunday, June 28
Shadow
Kalli Bidiyon: Malamin Ummulkhairi, Malar Makarantar da akawa kazafin satar yara a Maraban Jos, Ya canja baki a yanzu yace bai ga DPO ya mikawa mutane dalibar tasa ba

Kalli Bidiyon: Malamin Ummulkhairi, Malar Makarantar da akawa kazafin satar yara a Maraban Jos, Ya canja baki a yanzu yace bai ga DPO ya mikawa mutane dalibar tasa ba

Duk Labarai
An zargi Malamin Ummulkhairi, Malamar Makaranta a Maraban Jos da akawa kazafin satar yara da canja baki. A baya yace ya ga DPO ya mikawa mutane UmmilKhairi Amma a yanzu da aka mayar masa mashin dinsa yace bai ga DPO ba. https://www.tiktok.com/@jamilurabi/video/7655801179519208712?_r=1&u_code=ejaikd8elj8058&preview_pb=0&sharer_language=en&_d=ejaij098emc1h5&share_item_id=7655801179519208712&source=h5_m&timestamp=1782649783&user_id=7483197776647635989&sec_user_id=MS4wLjABAAAAN7fVbcc0mzRzgIxdVwTekj-Bzgfq381B8aILPWs15fqP6aFNZ5GwIpbLEwMTYvVW&item_author_type=2&social_share_type=0&utm_source=copy&utm_campaign=client_share&utm_medium=android&share_iid=7625183675001341712&share_link_id=2b60cf08-f818-4d08-a6cd-c5f977bc554f&am...

Kalli Bidiyon: Na baka kwana biyu ka fito ka janye maganarka ko mu nuna maka yanda kudin fasikanci ke aiki>>Khadija Me Numfashi ta gayawa Malamin da yace Momi Gombe da kudin fasikanci ta gina Masallaci

Duk Labarai
Tauraruwar fina-finan Hausa, Khadija MaiNumfashi ta baiwa Malamin da yace Abokiyar aikinta, Momi Gombe da kudin fasinkaci ta gina masallaci kwana biyu ya fito ya janye maganarsa ko su dauki mataki akansa. Ta wallafa hakane a shafinta na Tiktok inda ta yi tambayar cewa shin menene hukuncin yiwa mutum kazafi? https://www.tiktok.com/@khadija_mainumfashi1/photo/7656261820851735826?_r=1&_t=ZS-97aRRnTCTw5 https://www.tiktok.com/@engr.haarun.adam.bauchi/video/7655374073219829012?_r=1&u_code=ejaikd8elj8058&preview_pb=0&sharer_language=en&_d=ejaij098emc1h5&share_item_id=7655374073219829012&source=h5_m&timestamp=1782647437&user_id=7483197776647635989&sec_user_id=MS4wLjABAAAAN7fVbcc0mzRzgIxdVwTekj-Bzgfq381B8aILPWs15fqP6aFNZ5GwIpbLEwMTYvVW&it...
Kalli Bidiyon: Gwamnan jihar Kaduna, Malam Uba Sani ya kai ziyara gidan malamar da aka zarga da satar yara inda ya sha Alwashin kula da yaran data bari kamar nasa

Kalli Bidiyon: Gwamnan jihar Kaduna, Malam Uba Sani ya kai ziyara gidan malamar da aka zarga da satar yara inda ya sha Alwashin kula da yaran data bari kamar nasa

Duk Labarai
Gwamnan jihar Kaduna, Malam Uba Sani ya bayyana cewa, zai dauki nauyin 'ya'yan matarnan da aka yiwa kazafin satar yara a Maraban Jos Kaduna kamar 'ya'yansa. Ya bayyana hakane a yayin ziyarar ta'aziyya da jaje da ya kaiwa iyalan mamaciyar. Sannan yace an kama mutane 100 da hannu a lamarin inda yace guda 40 suna da hannu kai tsaye a lamarin sannan akwai sauran da ake zargi da yin gangamu ba bisa ka'ida ba. Yace zasu tabbatar an musu hukuncin da ya dace dan kada gobe ma wasu su kara. https://www.tiktok.com/@jkdmedia_/video/7656188486147394824?_r=1&_t=ZS-97aP4cm8ILg
Kalli Bidiyon: Zamanin da muke ciki ya karyata Hadisin dake cewa, Musulmi dan Uwan Musulmi ne>>Inji Mawaki Soja Boy

Kalli Bidiyon: Zamanin da muke ciki ya karyata Hadisin dake cewa, Musulmi dan Uwan Musulmi ne>>Inji Mawaki Soja Boy

Duk Labarai
Tauraron mawakin Hausa, Soja Boy ya bayyana cewa, zamanin da muke ciki ya karyata Hadisin dake cewa Musulmi dan uwan Musulmi ne. Soja boya yace watakila kuma karya akawa Annabi(Sallallahu Alaihi Wasallam) bai fadi hakan ba ko kuma Annabi(Sallallahu Alaihi Wasallam) idan ya fadi hakan yana nufin mutanen zamaninshi ne kawai ba hadda mu ba. Ya kawo dalilinsa na cewa Larabawa basa son bakar fata ko kadan, yace amma me yasa malamai suke cusawa Kabilar Hausa son Bakar fata? Yace amma kuma duk wani abu na Al'adar Hausa sai ace shi kuma bai dace ba. https://www.tiktok.com/@officialsojaboyy/video/7656179805678750996?_r=1&_t=ZS-97aNGHRd7Ky
Kalli Bidiyon Da Duminsa: Tauraron fina-finan Hausa, Musa Mai Sana’a ya kwanta rashin Lafiya

Kalli Bidiyon Da Duminsa: Tauraron fina-finan Hausa, Musa Mai Sana’a ya kwanta rashin Lafiya

Duk Labarai
Rahotanni sun bayyana cewa, Tauraron fina-finan Hausa, Musa Mai Sana'a ya kwanta rashin lafiya kuma jikin yayi tsanani. Kamar yanda Ahmad Nakowa Backup ya ruwaito, yace Jikin Mai Sana'a yayi tsanani. Saidai bai fadi kalar rashin lafiyar dake damunsa ba. https://www.tiktok.com/@ahmadnakowamhd/video/7656128961067437320?_r=1&_t=ZS-97a5WmQwTLs Musa Mai Sana'a dai yayi suna sosai wajan tallata Gwamnatin shugaban kasa, Bola Ahmad Tinubu.
Kalli Bidiyon: Dalilin da yasa kuka ga na daina Girgiza Nònò da Dùwàwù na samu mijin aurene, ina fatan Allah ya bani ‘ya’ya na gari>>Inji Me bakin Kyss

Kalli Bidiyon: Dalilin da yasa kuka ga na daina Girgiza Nònò da Dùwàwù na samu mijin aurene, ina fatan Allah ya bani ‘ya’ya na gari>>Inji Me bakin Kyss

Duk Labarai
Tauraruwar Tiktok, Me bakin Kiss ta bayyana cewa, kwana biyu da ta daina hawa shafinta tana girgiza Nono da Duwawu, ta samu mijin aurene. Tace a yanzu ta mayar da hankali wajan gyara tsakaninta da Ubangiji sannan kuma ko Miliyan daya za'a bata yanzu ba zata girgiza Nono da duwawu ba. Tace ita marainiyace ta fuskanci abubuwa daban-daban na kalubale amma yanzu duk abinda uba kewa dansa yanzu tawa kanta. https://www.tiktok.com/@mebakinkiss3/video/7656014894382320904?_r=1&_t=ZS-97a30bw7KEK
Kalli Bidiyon: Yanda dan Kwallon Najeriya, Victor Osimhen ya fito cikin dandazon matasa da suka zagaye motarsa suna rububin kallonsa yana musu gargadin kada su lalata masa motarsa ta Lamborghini

Kalli Bidiyon: Yanda dan Kwallon Najeriya, Victor Osimhen ya fito cikin dandazon matasa da suka zagaye motarsa suna rububin kallonsa yana musu gargadin kada su lalata masa motarsa ta Lamborghini

Duk Labarai
An ga dan kwallon Najeriya, Victor Osimhen ya fito daga motarsa da matasa suka zagaye yana gargadin su cewa, kada su lalata masa motarsa. Da yawa sun yi mamakin yanda ya fito cikin matasan ba tare da tsoro ba. https://twitter.com/i/status/2070754257024725099