Thursday, February 12
Shadow
Da Duminsa: Bayan da aka yi Yunkurin kamashi a filin Jirgi, EFCC tace ta aikawa Malam Nasiru Ahmad El-Rufai sammace

Da Duminsa: Bayan da aka yi Yunkurin kamashi a filin Jirgi, EFCC tace ta aikawa Malam Nasiru Ahmad El-Rufai sammace

Duk Labarai
Hukumar EFCC ta tabbatar da cewa, ta aikawa tsohon gwamnan jihar Kaduna, Malam Nasiru Ahmad El-Rufai sammacen ya bayyana a gabanta. Hakan na zuwane bayan da aka yi yunkurin kamashi a filin jirgi amma abu ya faskara. Rahotanni sun bayyana cewa, Lauyoyin EFCC ne suka tabbatar da hakan. Kuma sun ce, ElRufai ya amsa musu da cewa, zai bayyana a gaban EFCC din ranar Litinin.
Da Duminsa: Atiku Abubakar ya kaiwa Malam Nasiru Ahmad El-Rufai ziyara har gida bayan da aka yi yunkurin kamashi

Da Duminsa: Atiku Abubakar ya kaiwa Malam Nasiru Ahmad El-Rufai ziyara har gida bayan da aka yi yunkurin kamashi

Duk Labarai
Rahotanni sun bayyana cewa, tsohon mataimakin shugaban kasa, Alhaji Atiku Abubakar ya kaiwa tsohon Gwamnan jihar Kaduna, Malam Nasiru Ahmad El-Rufai ziyara a gidansa. Hakan na zuwane bayan da DSS suka yi yunkurin kama ElRufai a filin jirgin sama bayan da ya dawo Najeriya daga Egypt. Babu dai wani bayani game da ganawar tasu. Hakan na zuwane bayan da Rotimi Amaechi ya kaiwa ElRufai ziyara har gida inda shima ya nuna masa yana tare dashi.
Kalli Bidiyon: Sadiya Haruna ta bayyana abinda ta kama mijinta yanawa kawarta da shine ya hadasu fada har ya saketa

Kalli Bidiyon: Sadiya Haruna ta bayyana abinda ta kama mijinta yanawa kawarta da shine ya hadasu fada har ya saketa

Duk Labarai
Tauraruwar Tiktok, Sadiya Haruna, ta bayyana abinda ta kama mijinta, yanawa kawarta wanda hakan yasa suka yi fara har ya saketa. Sadiya Haruna tace ta kama mijinta abinda bai kamata ba da Ladingo. kamar yanda zaku ji a wannan Bidiyon nata. https://www.tiktok.com/@realmaryamebraheem0/video/7605773360152317202?_r=1&_t=ZS-93s247dfvKC
DSS sun bayyana sunan wanda ya kai musu korafi akan Tsohon Gwamnan Kaduna, Malam Nasiru Ahmad El-Rufai su bincikeshi

DSS sun bayyana sunan wanda ya kai musu korafi akan Tsohon Gwamnan Kaduna, Malam Nasiru Ahmad El-Rufai su bincikeshi

Duk Labarai
Hukumar 'yansandan farin kaya ta DSS ta sanar da cewa bata yi niyyar kama tsohon gwamnan jihar Kaduna, Malam Nasiru Ahmad El-Rufai ba a filin jirgin sama bayan da ya dawo daga kasar Egypt ba. DSS tace ta kwace fasfon ElRufai dan tilasta masa ya amsa gayyatar data masa ne. Tace hukumar yaki da rashawa da cin hanci ce ta gabatar mata da bukatar binciken ElRufai shiyasa take nemansa. Wata Majiya daga DSS dince ta shaidawa gidan talabijin na Arise TV hakan.
Da Duminsa: Na mayar da matata, Maryam Nicky Minaj >>Inji Gfresh Al-amin

Da Duminsa: Na mayar da matata, Maryam Nicky Minaj >>Inji Gfresh Al-amin

Duk Labarai
Tauraron Tiktok, Gfresh Al-amin ya bayyana cewa, ya mayar da matarsa, Maryam Nicki Minaj. Ya bayyana hakane a wani Bidiyo da ya wallafa a shafinsa na Tiktok wanda hutudole ya kallah. Yace Maryam ta gane kuskurenta kuma an yi magana ta hankali tsakaninsa da iyayenta. https://www.tiktok.com/@gfreshfanpage/video/7606025047706193160?_r=1&_t=ZS-93rmQL4usmf Kalli Bidiyon anan
Kalli Bidiyon: Kalaman Da Naja’atu ta yi akan Farfesa Isa Ali Pantami ya nuna cewa, bata san addini ba>>Inji Malam Abdulrahman Umar Sautussunnah

Kalli Bidiyon: Kalaman Da Naja’atu ta yi akan Farfesa Isa Ali Pantami ya nuna cewa, bata san addini ba>>Inji Malam Abdulrahman Umar Sautussunnah

Duk Labarai
Malam Abdulrahman Umar Sautussunnah ya mayarwa da Naja'atu martani kan kalaman da ta yi akan Farfesa Isa Ali Pantami. Naja'atu dai tace farfesa Makaryaci ne. Saidai a martanin Malam Abdulrahman Umar Sautussunnah yace hakan ya nuna bata san addi ba, dan akwai malaman addini da yawa dake bayar da fatawa su canja. https://www.tiktok.com/@izzalatul.bidia/video/7605988740774759700?_r=1&_t=ZS-93rhd2fTeW9
Kalli Bidiyon: Abinda Farfesa Isa Ali Pantami ya ce bayan kalaman da Najaatu ta yi akansa

Kalli Bidiyon: Abinda Farfesa Isa Ali Pantami ya ce bayan kalaman da Najaatu ta yi akansa

Duk Labarai
Bayan kalaman da Naja'atu ta yi akan Farfesa Isa Ali Pantami inda ta bayyanashi da makaryaci lamarin ya dumama kafafen sada zumunta. Wani Bidiyo ya bayyana inda aka ji Farfesa na cewa, Allah ne kadai zai yabi mutum ya daukaka ko kuma ya aibatashi ya kaskanta. Farfesa ya kara da cewa, idan mutum ya ga dama ya shiga BBC yayi ta zaginsa bai dameshi ba. Duk da be kama suna ba, da yawa sun fassara cewa, Martanine yawa Naja'atu. https://www.tiktok.com/@mudassirabdulrahm/video/7605857065675803912?_r=1&_t=ZS-93rfbSLtjlZ
Kalli Bidiyon Abinda DSS sukawa El-Rufai bayan da suka so kamashi a filin jirgi bayan da ya dawo daga kasar Egypt amma yaki yadda su kamashi

Kalli Bidiyon Abinda DSS sukawa El-Rufai bayan da suka so kamashi a filin jirgi bayan da ya dawo daga kasar Egypt amma yaki yadda su kamashi

Duk Labarai
Tsohon Gwamnan jihar Kaduna, Malam Nasiru Ahmad El-Rufai ya dawo daga kasar Egypt inda ya hadu da barazanar kame daga DSS a filin jirgi bayan da ya sauka a Najeriya. Saidai El-rufai yaki yadda yabi DSS din inda yace idan suna son gayyatarsa su aiko masa da takarda. Ya bayyana cewa ko shugaban kasa, bai isa yace masa ga abinda ya kamata yayi ba. Jama'a da yawa sun taru suka hana a tafi da malam Nasiru Ahmad El-Rufai inda suka ce sai ya je gida. A karshe, me magana da yawunsa, Muyiwa Adejobi ya bayyana cewa, DSS sun kwace fasfon ElRufai din. https://twitter.com/i/status/2021941497319317730
An bayyana sunayen wadanda suka zuga kasar Amurka ta hana Kwankwaso Visar shiga kasarta sannan ta kwace kadarorinsa

An bayyana sunayen wadanda suka zuga kasar Amurka ta hana Kwankwaso Visar shiga kasarta sannan ta kwace kadarorinsa

Duk Labarai
A jiyane ne dai kasar Amurka ta fara shirin daukar mataki kan hana wasu 'yan Najeriya Visa ta shiga kasarta da kuma keace kadarorinsu saboda zargin suna cikin masu dakile 'yancin yin addini. Daga cikin wadanda kasar ta Amurka zata dauki mataki akansu akwai tsohon gwamnan Kano, Dr. Rabiu Musa Kwankwaso. Da yake magana a wata hira da aka yi dashi. Na kusa da Kwankwaso, Injiniya Buba Galadima ya bayyana cewa, gidan talabijin na Arise TV, da gidan jaridar Thisday da wasu 'yan siyasa ne suka zuga kasar Amurka akan Kwankwaso. Yace ko maganar shari'a da aka yi a Arewa, Kwankwaso bai yi shari'ar Musulunci a Kano ba. https://twitter.com/i/status/2021895699424555332