Wednesday, April 15
Shadow
Da Duminsa: Ministan Tsaro, Christopher Musa ya fadi sunan masu daukar nauyin Tshàgyèràn Dhàjì

Da Duminsa: Ministan Tsaro, Christopher Musa ya fadi sunan masu daukar nauyin Tshàgyèràn Dhàjì

Duk Labarai
Ministan Tsaro, Christopher Musa ya bayyana cewa yana zargin 'yan siyasa na bangaren adawane ke daukar nauyin matsalar tsaro a kasarnan. Ya bayyana cewa suna yin hakanne kawai dan su nuna cewa Gwamnati ta gaza. Ya bayyana hakane a hirar da aka yi dashi a gidan talabijin na Arise TV. Yace idan aka lura duk idan zabe ya karato sai kaga matsalar tsaro tana ta'azzara. Yace ba sai mutum yabi ta wannan hanyar ba sannan zai samu mulki.
Da Duminsa: Shugaba Tinubu yayi magana akan Shigar da Dino Melaye yayi zuwa wajan babban taron jam’iyyar ADC

Da Duminsa: Shugaba Tinubu yayi magana akan Shigar da Dino Melaye yayi zuwa wajan babban taron jam’iyyar ADC

Duk Labarai
Fadar shugaban kasa ta yi magana akan shigar da Dino Melaye yayi ya je wajan babban taron jam'iyyar ADC. Shugar ta Dino Melaye ta dauki hankula sosai a kafafen sada zumunta inda ake ta muhawara akai. Me magana da yawun shugaban kasa, Bayo Onanuga ya bayyana cewa, Dino Melaye shine daya daga cikin mashirmatan shuwagabannin jam'iyyar ADC. Yace Allah ya mana tsari daku. https://twitter.com/i/status/2044525281021419721
Da Duminsa: Gwamnatin tarayya ta bayyana jihohi 33 da kananan hukumomi 226 dake fuskantar yiyuwar Ambaliyar ruwa a Najeriya

Da Duminsa: Gwamnatin tarayya ta bayyana jihohi 33 da kananan hukumomi 226 dake fuskantar yiyuwar Ambaliyar ruwa a Najeriya

Duk Labarai
Gwamnatin tarayya ta bayyana jihohi 33 da kananan hukumomi 226 da ke fuskantar barazanar Ambaliyar ruwa a damunar bana. Ministan ruwa da tsafta, Joseph Utsev ne ya bayyana hakan a yayin ganawa da manema labarai a Abuja. Ya bayyana cewa, Jihohin da Ambaliyar ruwan zata faru sun hada da Abia, Adamawa, Anambra, Bauchi, Bayelsa, Benue, Borno, Cross River, Delta, Ebonyi, Edo, Enugu, Gombe, Imo, Jigawa, Kaduna, Kano, Kebbi, Kogi, Kwara, Lagos, Nasarawa, Niger, Ogun, Ondo, Osun, Oyo, Plateau, Rivers, Sokoto, Taraba, Yobe, Zamfara, da babban birnin tarayya, Abuja. Ya bayyana cewa wasu garuruwan akwai hatsari me yawa wasu kuma kadan na faruwar ambaliyar ruwan.
Da Duminsa: Kasar Amurka tace shugaba Tinubu ya gaggauta cire karamin Ministan tsaro, Bello Matawalle daga mukaminsa saboda bata yadda dashi ba

Da Duminsa: Kasar Amurka tace shugaba Tinubu ya gaggauta cire karamin Ministan tsaro, Bello Matawalle daga mukaminsa saboda bata yadda dashi ba

Duk Labarai
Kasar Amurka ta bayyana cewa bata yadda da karamin ministan tsaro na Najeriya ba, Bello Matawalle. 'Yar majalisar jihar Florida, Kimberly Daniels ce ta bayyana hakan inda tace suna kira ga shugaban kasa, Bola Ahmad Tinubu ko dai ya cire Bello Matawalle ko kuma ya canja masa ma'aikata. Hakan na zuwane yayin da matsalar tsaro ke ci gaba da ta'azzara a musamman Arewacin Najeriya. A baya dai akwai zarge-zargen da ake tawa karamin Ministan tsaron wanda ya sha musantawa
Nafiu Bala Gombe ya samu matsala da masu daukar nauyinsa

Nafiu Bala Gombe ya samu matsala da masu daukar nauyinsa

Duk Labarai
Rahotanni sun bayyana cewa, Nafiu Bala Gombe da ya fito yace shine shugaban jam'iyyar ADC na riko ya kawo tarnaki a jam'iyyar ya samu matsala da masu daukar nauyinsa. Rahoton yace dama rabin kudin aiki aka bashi idan ya kammala za'a bashi sauran amma yanzu ya nemi a bashi sauran amma sun kiya Saboda sun ce ya kasa hana a yi babban taron jam'iyyar na ADC. Hakanan dakin Otal Din da suke biya masa a Transcorp Hilton sun daina biya Rahoton yace sun babe sosai.
Kalli Bidiyon: An tambayi Atiku Abubakar shin zai iya janyewa Peter Obi idan ya ga cewa ya fishi jama’a?

Kalli Bidiyon: An tambayi Atiku Abubakar shin zai iya janyewa Peter Obi idan ya ga cewa ya fishi jama’a?

Duk Labarai
A wata hira da aka yi da tsohon mataimakin shugaban kasa, Alhaji Atiku Abubakar, an tambayeshi shin zai iya janyewa Peter Obi takara idan ya lura Peter Obin yafi shi jama'a? Atiku yace zai iya mana. Yace ita takarar siyasa ana samuntane ta hanyar zaben fidda gwani ko kuma ta hanyar samar da dan takara na bai daya. Yace a kowane mataki idan Peter Obi ya zamana shine yayi nasara zai goyi bayansa. https://twitter.com/i/status/2044467777180672111
Tattalin arzikin Najeriya zai samu habaka fiye daga kasashen Amurka, Ingila, da Jamus>>Inji Fadar shugaban kasa

Tattalin arzikin Najeriya zai samu habaka fiye daga kasashen Amurka, Ingila, da Jamus>>Inji Fadar shugaban kasa

Duk Labarai
Fadar shugaban kasa, ta bayyana cewa, Tattalin arzikin Najeriya zai samu habaka sosai fiye dana kasashe masu arziki irin su Amurka, Ingila, da Jamus. Me magana da yawun shugaban kasa, Daniel Bwala ne ya bayyana haka a wata sanarwa da ya fitar ta shafinsa na X inda yake martani kan bayanan habakar tattalin arziki da kungiyar bayar da lamuni ta Duniya, IMF ta fitar. IMF tace Najeriya zata samu habakar tattalin arziki da maki 4.1 a shekarar 2026. Wannan maki yafi na kasar Amurka wanda IMF tace 2.3 ne sannan yafi na kasar Ingila wanda IMF tace 0.8 ne hakanan yafi na kasar Jamus wanda shima 0.8 ne. Daniel yace Gwamnatin Tinubu ba da wasa take ba.
Matsalar tsaron Arewa ta kai matsayin Yaqi>>inji Kungiyar Tuntuba ta Arewa

Matsalar tsaron Arewa ta kai matsayin Yaqi>>inji Kungiyar Tuntuba ta Arewa

Duk Labarai
Kungiyar tuntuba ta Arewa, ACF ta bayyana cewa, matsalar tsaron da ake fama da ita ta kai matsayin yaki. Kungiyar tace tana kira ga Gwamnati data karkatar ta hankalinta da ma dukkan wani abu daya shafi kudi dan ganin an magance wannan matsala. Kungiyar ta bayyana matsayar tane bayan zaman data yi. Zaman ya samu halartar Tsohon shugaban sojoji, Janar Tukur Yusuf, Da Tsohon shugaban 'yansanda, Muhammad Abubakar, da tsohon sakataren majalisar Dinkin Duniya, Tijjani Muhammad-Bande, da tsohon sakataren gwamnatin tarayya, Mahmud Ahmad, da shugaban kungiyar, Bashir Dalhatu. Sun bayyana cewa matsalar tsaron na jefa musamman yankin Arewa cikin tawayar tattalin arziki da kuma daidaita iyalai da sauransu.
Da Duminsa: Bayan Nafiu Bala Gombe, Jam’iyyar ADC ta sake korar karin wasu mutane daga cikinta

Da Duminsa: Bayan Nafiu Bala Gombe, Jam’iyyar ADC ta sake korar karin wasu mutane daga cikinta

Duk Labarai
jam'iyyar ADC ta fitar da cikaken bayanin mutanen daga kora daga jam'iyyar inda ta bayyana cewa maciya amana ne kuma sunawa jam'iyyar zagon kasa. Jam'iyyar tace ta dauki wannan mataki ne a babban taronta na kasa data gudanar a Abuja, kamar yanda me magana da yawun jam'iyyar, Bolaji Abdullahi ya sanar. Wadanda aka kora din sune kamar haka, Hon. Leke Abejide, Nafiu Bala Gombe, Mr. Kingsley Temitope Ogga, Mr. Don Norman Obinna, Mr. Kennedy Odion, Mr. Clement Ehigiator, Mrs. Stella Chukwuma, Patrick Ambut, Johny Tovie Derek, Duke Dick, and Elias Adikwu.
Me ya Faru? Malam Nasiru Ahmad El-Rufai zai ci gaba da zama a hannun ICPC duk da kotu ta bayar da belinsa

Me ya Faru? Malam Nasiru Ahmad El-Rufai zai ci gaba da zama a hannun ICPC duk da kotu ta bayar da belinsa

Duk Labarai
Rahotanni sun bayyana cewa, tsohon Gwamnan kaduna, Malam Nasiru Ahmad El-Rufai zai ci gaba da zama a hannun hukumar ICPC duk da cewa kotu ta bayar da belinsa. Mai shari'a na babbar kotun tarayya dake Kaduna, Justice Rilwanu Aikawa ne ya bayar da belin malam Nasiru Ahmad El-Rufai a ranar Talata. Bayan bayar da belin nasa, El-Rufai yaki yin magana da manema labarai amma wani na kusa dashi ya shaidawa jaridar Daily Trust cewa, kotu ta saka sharuda 10 akan belin na Malam Nasiru Ahmad El-Rufai. Yace sai an cika wadannan sharudanne sannan za'a sakeshi.