Monday, April 13
Shadow
Da Duminsa: Wata Sabuwa Wani me suna Hon. Muh’d Raji Sulaiman Zumo ya bayyana cewa, Shine shugaban jam’iyyar ADC na jihar Adamawa kuma ya dakatar da Atiku Abubakar da Babachir David Lawal

Da Duminsa: Wata Sabuwa Wani me suna Hon. Muh’d Raji Sulaiman Zumo ya bayyana cewa, Shine shugaban jam’iyyar ADC na jihar Adamawa kuma ya dakatar da Atiku Abubakar da Babachir David Lawal

Duk Labarai
Wani me sunan Hon. Muh'd Raji Sulaiman Zumo ya bayyana a jihar Adamawa inda ya bayyana cewa, shine shugaban jam'iyyar ADC na jihar. Hakanan ya bayyana cewa ya dakatar da Atiku Abubakar da kuma Babachir David Lawal da sauran wasu 'yan jam'iyyar ADC din ta jihar Adamawa. https://twitter.com/i/status/2043733152972025887
Kalli Bidiyon: A yau ma Malam Nasiru Ahmad El-Rufai ya bayyana a gaban kotu

Kalli Bidiyon: A yau ma Malam Nasiru Ahmad El-Rufai ya bayyana a gaban kotu

Duk Labarai
Tsohon Gwamnan jihar Kaduna, Malam Nasiru Ahmad El-Rufai ya bayyana a gaban babbar kotun jihar Kaduna inda ake ci gaba da shari'arsa. Ana tsammanin Kotun zata yi hukunci game da neman belin da El-Rufai yayi. Duk da yana daure, a yau, Malam Nasiru Ahmad El-Rufai yayi magana akan babban tarin jam'iyyar ADC, watau Convention. https://twitter.com/i/status/2043641829753602147
Rikicin jam’iyyar ADC ya munana a jihar Adamawa tsakanin Binani da Babachir

Rikicin jam’iyyar ADC ya munana a jihar Adamawa tsakanin Binani da Babachir

Duk Labarai
Rahotanni daga jihar Adamawa na cewa, rikicin jam'iyyar ADC ya munana tsakanin Aishatu Dahiru Binani da Babachir David Lawal. Rikicin yayi kamari ta yanda yanzu haka Binani da Elisha Abbo zasu yi zama da magoya bayansu dan yanke shawarar ci gaba da zama ko ficewa daga jam'iyyar ADC. Hakan na zuwane yayin da magoya bayan Binani ke ta kira a gareta da cewa, ta fice daga jam'iyyar ta ADC. Magoya bayan Binani na cewa, shekaru 10 tana rike da jam'iyyar amma gashi daga baya su Babachir sun zo zasu kawo tarnaki. Yanzu dai abin jira shine a ga matakin da Binani zata dauka
Kalli Bidiyon: Ta Fadan Cacar baki ya barke tsakanin Atiku Abubakar da Kashim Shettima

Kalli Bidiyon: Ta Fadan Cacar baki ya barke tsakanin Atiku Abubakar da Kashim Shettima

Duk Labarai
Fadan cacar baki ya barke tsakanin tsohon Mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar da mataimakin shugaban kasa, Kashim Shettima. Kashim Shettima ne ya fara tsokana inda yace Atiku ya fadi ayyuka 8 na ci gaba da yayi a Arewa da mutane 8 da ya taimaka a Arewa. Saidai a martaninsa, Atiku yace wannan rashin kunyane, Kashim Shettima bashi da kunya, domin a girme, ya girmeshi bai kamata ya kalleshi ya rika gaya masa irin wannan maganar ba. Sannan yace ba zai bashi amsa ba. Atiku yace idan ma aikin Gwamnati ne, yafi Kashim Shettima iyawa da Kwarewa. https://twitter.com/i/status/2043456696903680318
Maimakon Zagina, A samu wani yayi taimakon Musulunci ya aureni>>Inji Hafsee

Maimakon Zagina, A samu wani yayi taimakon Musulunci ya aureni>>Inji Hafsee

Duk Labarai
Tauraruwar Tiktok me amfani da sunan Hafseey ta bayyana cewa a daina Zaginta. Tace maimakon zagin da ake mata, me zai hana a samu wani yayi taimakon Musulunci ya aureta? Ta bayyana hakane a shafin nata na Tiktok inda tace duk wanda yasan da gaske yake kuma yana da sana'a ya fito ya mata magana da DM. https://www.tiktok.com/@hafseeyyarmalam1/video/7627408585479245077?_r=1&_t=ZS-95U0PZLKaaf
Da Duminsa: Ganduje da Doguwa sun bayyana wanda suke son a baiwa mataimakin gwamnan jihar Kano

Da Duminsa: Ganduje da Doguwa sun bayyana wanda suke son a baiwa mataimakin gwamnan jihar Kano

Duk Labarai
Dan majalisar Wakilai, Alhassan Ado Doguwa da Tsohon shugaban jam'iyyar APC, Dr. Abdullahi Umar Ganduje sun bayyana wanda suke so a baiwa Mataimakin Gwamnan jihar Kano. Duka su biyun sun bayyana Murtala Garo a matsayin wanda suke son a baiwa mataimakin Gwamnan jihar ta Kano. Doguwa ya bayyana hakane a wata sanarwa da ya fitar ranar Lahadi a Abuja. Rahoton yace an cimma matsayar a zabi garo a matsayin mataimakin Gwamnan jihar Kano ne bayan wani zama da masu fada aji na jam'iyyar APC a jihar Kano suka yi ranar Asabar. Kuma kaso 90 cikin 100 na mutanen suka ce sun amince a zabi Garo a matsayin mataimakin gwamnan jihar.
Da Duminsa: Kun dai san ni Sanata ne koh? Toh wallahi tunda Tinubu ya zama shugaban kasa, babu kasafin kudin da aka aiwatar sacw kudin kawai suke>>Inji Sanata Aminu Waziri Tambuwal

Da Duminsa: Kun dai san ni Sanata ne koh? Toh wallahi tunda Tinubu ya zama shugaban kasa, babu kasafin kudin da aka aiwatar sacw kudin kawai suke>>Inji Sanata Aminu Waziri Tambuwal

Duk Labarai
Sanata Aminu Waziri Tambuwal tsohon Gwamnan jihar Sokoto ya bayyana cewa, kasafin kudin shekarar 2023, dana 2024 dana 2025 duk ba'a aiwatar dasu ba. Yace Sace kudin kawai suke. Ya bayyana hakane a kan wani dandamali inda yake wa jama'a jawabi. Bidiyon jawabin nasa ya watsu sosai a kafafen sada zumunta. https://twitter.com/i/status/2043350800794079279
Kalli Bidiyon: Yanda wata Uwar Ango daga Arewa ta baiwa Amarya kyautar Fan Miliyan 10, kwatankwacin Naira Biliyan 25 kenan a matsayin Budan kai

Kalli Bidiyon: Yanda wata Uwar Ango daga Arewa ta baiwa Amarya kyautar Fan Miliyan 10, kwatankwacin Naira Biliyan 25 kenan a matsayin Budan kai

Duk Labarai
Wannan Bidiyon ya dauki hankula a kafafen sada zumunta sosai inda aka ga mahaifiyar Ango daga Arewa ta baiwa Amarya Fan Miliyan 10, kwatankwacin Naira Biliyan 25 kenan. Lamarin ya dauki hankula kuma ya jawo cece-kuce inda ake ta bayyana mamaki da faruwar hakan. Wasu kuma sun ce hakan Almubazzaranci ne. https://twitter.com/i/status/2043223867833942266