Saturday, July 4
Shadow
Wata Sabuwa: Dan Gwamnan jihar Anambra, Ozonna Charles Soludo ya zagi mahaifinsa

Wata Sabuwa: Dan Gwamnan jihar Anambra, Ozonna Charles Soludo ya zagi mahaifinsa

Duk Labarai
Rahotanni sun bayyana cewa, dan gwamnan jihar Anambra, Ozonna Charles Soludo ya zagi mahaifin nasa Ozonna ya hau wata waka inda ake zagin shugaban kasa, Bola Ahmad Tinubu da Mataimakin shugaban kasar, Kashim Shettima da mahaifinsa, Gwamnan jihar Anambra, Charles Soludo. An ganshi yana rawa yana bi yana rera wakar. Da yawa dai sun yi mamaki inda ake cewa ya kunyata Mahaifin nasa ba kadan ba. https://twitter.com/i/status/2073430642008764897
Kalli Bidiyon: Matashi ya samu yabo sosai saboda yanda ya tsaya gaban Sanata garinsu yake gaya masa cewa bai tsinana musu aikin komai ba

Kalli Bidiyon: Matashi ya samu yabo sosai saboda yanda ya tsaya gaban Sanata garinsu yake gaya masa cewa bai tsinana musu aikin komai ba

Duk Labarai
Wannan wani matashine daga jihar Kebbi da ya tsaya a gaban sanatansu na Yauri, Hon. Garba Musa Maidoki yake gaya masa cewa bai musu aikin komai ba. Yace ko aikin Miliyan 50 sanatan bai yi ba a mazabarsa wanda zasu iya nunawa su ce a zabeshi saboda shi. Yace da yawansu masu yada manufar sanatan a kafafen sada zumunta ba sa iya wallafa abinda sanatan ke yi saboda saidai su yi karya. https://twitter.com/i/status/2073334098806907385
Kalli Bidiyon Tonon Silili: An jiyo Isa Ashiru dan takarar gwamna na jam’iyyar ADC a jihar Kaduna yana zagin Malam Nasiru Ahmad El-Rufai

Kalli Bidiyon Tonon Silili: An jiyo Isa Ashiru dan takarar gwamna na jam’iyyar ADC a jihar Kaduna yana zagin Malam Nasiru Ahmad El-Rufai

Duk Labarai
Wata murya data bayyana a kafafen sada zumunta wadda aka bayyana cewa ta dan takarar Gwamnan jihar Kaduna ne Karkashin jam'iyyar ADC, Isa Ashiru an ji yana murna da kama Malam Nasiru Ahmad El-Rufai. Sannan ya bayyana cewa bai yafewa El-Rufai din ba kuma kamun da aka masa, Sakamakon abinda ya musu ne ya fara gani tun a Duniya kamin aje Lahira. Ya bayyana cewa shi dama neman takara ce ta kaishi jam'iyyar ADC. https://twitter.com/i/status/2073396042729459943
Kalli Bidiyon: Yanda wasu mata daga Arewa ke Sumhbatar Juna da Rungume-Rungume ya jawo musu cece-kuce

Kalli Bidiyon: Yanda wasu mata daga Arewa ke Sumhbatar Juna da Rungume-Rungume ya jawo musu cece-kuce

Duk Labarai
Wannan wasu mata ne daga Arewacin Najeriya da suka dauki hankula a kafafen sada zumunta bayan da aka gansu suna sumbatar juna suna rungumerungume a shafinsu na sada zumunta. Da yawa dai na zarginsu da Madigo duk da yake cewa su basu bayyana cewa suna aikata hakan ba. Daga cikin wadanda suka musu wannan zargi hadda Gfresh. https://www.tiktok.com/@ummilafi/video/7657472452385131796?_r=1&_t=ZS-97kOJjLJvkr https://www.tiktok.com/@gfreshfanpage/video/7658579608228482311?_r=1&_t=ZS-97kOnX0NTHR
Kalli Bidiyon: Bayan Ficewar Rabiu Rikadawa daga tafiyar Rarara, Yaron Rarara, Usman A. Adam ya bayyana cewa rashin gaskiyar da Baba Dan Audu ke yi ne a fim yake son yi musu shiyasa aka samu matsala dashi

Kalli Bidiyon: Bayan Ficewar Rabiu Rikadawa daga tafiyar Rarara, Yaron Rarara, Usman A. Adam ya bayyana cewa rashin gaskiyar da Baba Dan Audu ke yi ne a fim yake son yi musu shiyasa aka samu matsala dashi

Duk Labarai
Baba Dan Audu, Watau Rabiu Rikadawa ya sanar da ficewa daga tafiyar Dauda Kahutu Rarara. Saidai bayan ficewarsa, daya daga cikin yaran Rarara, Usman A. Adam ya bayyana cewa, Rashin gaskiyar da yake yi ne a film yaso yi musu shiyasa aka samu matsala dashi. Kuma Usman ya rika kiran Baba Dan Audu da Barawo. https://www.tiktok.com/@horonzango/video/7658364588173430034?_r=1&_t=ZS-97kMOO5quZB A wata hira da DCLHausa ta yi dashi, Rikadawa yace Naira Miliyan 200 gwamnatin jihar Gombe ta basu a ziyarar da suka kai. Saidai ba Rikadawa ne kadai ya fice daga tafiyar Rarara ba akwai irinsu Mansurah Isah da Fati KK.
Kalli Bidiyon: An gano mata masu dauke da cikin Shyege a cikin matan da gwamnatin Kano Zatawa auren gata

Kalli Bidiyon: An gano mata masu dauke da cikin Shyege a cikin matan da gwamnatin Kano Zatawa auren gata

Duk Labarai
Rahotanni daga jihar Kano na cewa, An gano cewa wasu daga cikin matan da gwamnatin jihar zatawa Auren gata suna dauke da juna biyu. Hakan yasa dole aka daga maganar auren inda aka cire wadanda aka samu da cikin ake neman wasu su maye gurbinsu. https://www.tiktok.com/@fahadkabirmaitata/video/7658457409010093333?_r=1&_t=ZS-97kL661uAce
Kalli Bidiyon: Yanda Gwamnan Kano, Abba Kabir Yusuf da Mataimakinsa, Sule Garo suka je fadar Sarkin Kano aka yi zikirin shekara dasu

Kalli Bidiyon: Yanda Gwamnan Kano, Abba Kabir Yusuf da Mataimakinsa, Sule Garo suka je fadar Sarkin Kano aka yi zikirin shekara dasu

Duk Labarai
Gwamnan Kano, Abba Kabir Yusuf da mataimakinsa, Murtala Sule Garo sun je fadar Sarkin Kano, Me martaba Muhammad Sanusi II inda aka yi zikirin shekara dasu. Sannan an yiwa Najeriya Addu'ar ci gaba da zaman lafiya a wajan. An yi zikirinne a jiya Juma'a. https://www.tiktok.com/@kanoemiratecouncil/video/7658365568965201173?_r=1&_t=ZS-97kK6VuKTfp