Tuesday, July 14
Shadow
Me sayar da kosai akan Naira dubu ashirin da biyu

Me sayar da kosai akan Naira dubu ashirin da biyu

Duk Labarai
Wata mata ta bayyana a Legas dake sayar da kosanta akan Naira 22,000. Matar dai a Lekki take kuma sunan wajan sayar da kosan nata The Akara Lekki. Lamarinta ya dauki hankula a kafafen sada zumunta saboda an saba sayen Kosai akan Naira 50 zuwa 100 amma nata ya zo da farashi me tsada. A kariyar data rika baiwa kanta, matar tace, kosanta ba irin na sauran bane, ba kosai bane kawai, takan saka kifi, Nama hadda ma kaza a ciki. Sannan wajanta akwai tsafta, hakanan unguwar da take Lekki babbar unguwa ce wadda kama shago na da tsada.
Kalli Bidiyon: Ban yadda Allah yace a aika wanda ya bar musulunci Kiyama ba hakanan ban yadda Allah na saukar da bala’i daga sama ba>>Inji Mawaki Soja Boy

Kalli Bidiyon: Ban yadda Allah yace a aika wanda ya bar musulunci Kiyama ba hakanan ban yadda Allah na saukar da bala’i daga sama ba>>Inji Mawaki Soja Boy

Duk Labarai
Tauraron mawakin Hausa, Soja Boy ya bayyana cewa, bai yadda Allah ne yace duk wanda ya bar Musulunci ba a aikashi kiyama ba. Yace hakanan bai yadda Allah ne ke saukar da bala'i ba. Ya bayyana hakane a wata hira da aka yi dashi a TiktokLive. Soja Boy yace Malaman Najeriya ba daidai suke fassara Qur'ani ba. https://www.tiktok.com/@abbakar_abaya_kano1/video/7661820085514046741?_r=1&_t=ZS-981JZsAlAXw
Daya daga cikin yaran Atiku ya zargi Aslam Aliyu da tace zatawa Atiku Tonon silili da daukar daya daga cikin shahararrun mawakan Arewa tana zuwa kasashen Turawa dashi

Daya daga cikin yaran Atiku ya zargi Aslam Aliyu da tace zatawa Atiku Tonon silili da daukar daya daga cikin shahararrun mawakan Arewa tana zuwa kasashen Turawa dashi

Duk Labarai
Aslam Aliyu da ta fita daga ADC ta kusa da Atiku ta koma APC na ci gaba da shan suka daga wasu daga cikin yaran Atiku. Aslam ta yi gargadin cewa idan ba'a daina sukarta kan ficewa daga APC ba, zata fasa kwai akan Atiku wanda ba zaiwa kowa dadi ba. Saidai a martani ga wannan maganar, daya daga cikin yaran Atiku ya fito yace ya baiwa Aslam Awanni ta fito ta fasa kwan da tace akan Atiku. Inda ya zarge ta da yawo da daya daga cikin shahararrun matasan mawakan Arewa, yace tana daukarsa zuwa kasa-kasa suna yawon shakatawa. Ya wallafa cewa zasu bayyanawa Duniya abinda Aslam take aikatawa da mawaki Salim Smart. Sannna ya wallafa wannan Rubutun: Dr Aslam Mun San Abunda Kike Boyewa Duniya Akan Salim Smart Da Wasu Abubuwan, Idan Baki Fasa Kwai Ba Mu Zamu Fasa Naki Kwan, Atiku Ba...
Kalli Bidiyon: Yanda yaran Rarara sukawa Mansurah Isah Dibar Albarka suka fitar da update dinta

Kalli Bidiyon: Yanda yaran Rarara sukawa Mansurah Isah Dibar Albarka suka fitar da update dinta

Duk Labarai
A yayin da ake yakin cacar baki tsakanin Tauraruwar fina-finan Hausa, Mansurah Isah da Rarara da Matarsa A'ishatulhumaira bayan da Mansuran ta fita daga Tafiyar Triple R. Wasu mata yaran Rarara sun fito sun saki Update din Mansurah Isah. A baya dai Mansurah Isah ta fice daga tafiyar Rarara ta Triple R, saida wasu Rahotanni sun fito sun bayyana cewa ta koma tafiyar. Saidai Kwatsam ana kan hakane sai ga Mansurah Isah ta sake fitowa tace ta bar Tafiyar Rarara ta Triple R kuma ta musu alkawarin ba zata yi hira da 'yan jarida ba. Tace amma taga ana tura yara suna mata rashin Kunya a kafafen sadarwa inda ta gargadi Rarara da matarsa A'ishatulhumaira inda tace idan aka fara tone-tone abin ba zaiwa kowa dadi ba. A'ishatulhumaira, matar Rarara ta mayarwa da Mansurah Isah da martanin ...
Wata Sabuwa: Reshe ya juye da mujiya, An kama mijin nan da ya zargi malamin jami’a a Kano da neman matarsa, itama matar an kamata

Wata Sabuwa: Reshe ya juye da mujiya, An kama mijin nan da ya zargi malamin jami’a a Kano da neman matarsa, itama matar an kamata

Duk Labarai
Rahotanni daga Kano na cewa, jami'an tsaro sun kama mijin matarnan da ya zargi malamin jami'a a Kano da neman matarsa har ya tara mutane suka lakadawa malamin na jaki. Itama Matar an kamata ana bicikensu. Malamin ne ya shaidawa manema labarai na gidan Radio din Freedom hakan a wata hira da suka yi dashi. Yace ya kai korafi ofishin 'yansanda kan Abinda aka masa, shine aka gayyaci matar da mijinta ake bincikensu. A cikin hirar da aka yi dashi yace tunda yake bai taba aikata, Zyna ba.