Farashin dala a kasuwar Gwamnati ta yau, Litinin 20, ga watan Aprilu na shekarar 2026 ya kama akan Naira 1,347.33 duk wata.
A kasuwar bayan fage ta garuruwan Kano, Legas da Abuja kiwa ana sayen dalar akan Naira 1,395, inda ake sayar da ita akan Naira 1405
Wani malami da ya je koyar da dalibai a jami'ar Federal University Kashere dake jihar Gombe ya bayyana cewa ya je ya iske ajin ba kowa.
Ya dauki Bidiyon ajin inda aka ga kujeru inda yace zai koma ofis ya tafi gida.
https://www.tiktok.com/@amedkt1/video/7630389740956634389?_r=1&_t=ZS-95gGL3UR7Wz
Rahotanni sun bayyana cewa, Gwamnatin tarayya ta karbi bashin Naira Biliyan 100 daga asusun bankunan 'yan Najeriya wadanda ba'a amfani dasu, wanda a turance ake kira da Dormant account.
Hakanan ta dauki kudaden daga ribar kamfanoni wadda mutane masu hannun jari a kamfanonin basu karbaba wadda a turance ake kira da Dividend.
Wata dokar kudi da aka yi a shekarar 2020 ce ta baiwa Gwamnatin tarayya damar rantar irin wadannan kudade.
A dazu ne dai muka di wani Dr. Adam ya koka cewa dan takarar Gwamnan jihar Gombe, Farfesa Ali Pantami ya yi Blocking dinsa saboda ya gaya masa gaskiya a cewar Adamu
A yanzu kuwa watace itama me suna Huraira ta roki mallam ya bata Miliyan 2 ta ja jari bayan ta ganshi a jirgin sama.
Saidai itama yayi Blocking dinta.
A karshe dai ta roki malam ko dubu dari biyu ya bata.
https://twitter.com/i/status/2045896467609420011
Tsohon Gwamnan Kaduna, Malam Nasiru Ahmad El-Rufai ya bayyana wata Mqarqashiya da yace ana shirya masa dan ci haba da tsareshi na tsawon lokaci.
Ya bayyana hakane ta bakin me magana da yawunsa, Muyiwa Adekeye inda yace Jaridar The Nation ta ruwaito cewa, wai daya daga cikin masu bayar da shaida akansa me suna Mohammed Umar Karage 'yan Bindiga sun shiga gidansa.
Ya zargi cewa harin da aka kai masa bai rasa nasaba da shaidar da yake bayarwa akan malam Nasiru Ahmad El-Rufai.
Dan hakane Malam Nasiru Ahmad El-Rufai yace wannan bata sunane kuma ya baiwa lauyoyinsa umarnin su kai karar gidan jaridar.
Ya bayyana cewa bashi da hannun a harin da aka kaiwa shaidar nasa dan shi mutum ne me son bin doka da oda.
Wannan wani matashine dake koya Jyma'i a Tiktok da kuma kalaman batsa kala-kala.
Saidai dubunsa ta cika bayan da wansa ya kamashi ya masa na jaki sannan yayi Alkawarin ba zai kara ba.
https://www.tiktok.com/@bakeer.rb/video/7629809686136524048?_r=1&_t=ZS-95fclwMA4Yr
Wannan wani Ango ne da gaban rigarsa ya tashi a wajan da ake shagalin aurensa.
Lamarin ya dauki hankula sosai inda wasu ke zargin cewa wai ya sha maganin karfin maza ne.
Wasu kuma na cewa iska ce ta hura rigarsa.
https://twitter.com/i/status/2045826232533602784
Wata 'yar Tiktok me suna Zainab ta bayyana cewa duk da tana Musulma, idan ta samu Me sonta Kirista, zata bishi.
Ta yi tambayar cewa shin akwai adalci a tsarin cewa Musulmi zai auri Kirista mace amma ita mace musulma ba zata iya auren Kirista namiji ba?.
https://www.tiktok.com/@zainab00670/photo/7629070664762232071?_r=1&_t=ZS-95fayCgdHn7
Me amfani da kafafen sada zumunta, Dr. Adam Umar ya bayyana cewa, daga ya gayawa farfesa Isa Ali Pantami Gaskiya kawai sai ya yi Blocking dinsa.
Ya bayyana hakane a shafinsa na X
Ya ga wani Bidiyon Sheikh Pantami a jirgin sama ne shine ya rubuta masa:
"hmmm Allah sarki duniya. Duk abubuwan yan siyasa din da kakeyin hani da shi kayi. Private jet shatter the cheapest fare is 10,000$ (abt 14million), a journey that u can do with just about 300k naira. Even if it was paid for u, the mallam we know in the past could reject it bt hmm"
https://twitter.com/i/status/2045367705113383111
Saidai yace bayan Hakan, Pantami yayi Block dinsa
https://twitter.com/i/status/2045494899953283400
Yace abinnya matukar bashi mamaki.
Wannan Ministan babban birnin tarayya, Abuja Nyesom Wike ne ya fashe da kuka a coci
Yana kukanne yayin da ake jana'izar wani abokinsa da ya rigamu gidan gaskiya.
https://www.tiktok.com/@chinwiben.web3/video/7629087800146611474?_r=1&_t=ZS-95eAltjMpY8