Wannan wata matace data bayyana a kafafen sada zumunta tace shekarunta 41 kuma tana neman mijin aure.
Ta sha Alwashin duk wanda ya yadda ya aureta, zata bashi kyautar Naira Miliyan 10.
https://twitter.com/i/status/2077694292169015703
A yayin da yake jiran wasansu na karshe da kasar Argentina.
An ga dan wasan Spain, Lamine Yamal ya fita a birnin New York na kasar Amurka ya nemo abinci halal ya siyasa.
An ganshi tare da Budurwarsa da me bashi tsaro.
https://twitter.com/i/status/2078016891558224135
Wani abu me kama da Kumfa ko Gajimare daya bayyana a kusa da garin Jere dake kan hanyar Abuja zuwa Kaduna ya dauki hankula.
https://www.tiktok.com/@trtafrikaha/video/7663168985520753928?_r=1&_t=ZS-985kIkkmpXU
Ba'a san dalilin bayyanar abin ba
Mutane sun taru sunata kallonsa suna mamaki.
https://www.tiktok.com/@trtafrikaha/video/7663168985520753928?_r=1&_t=ZS-985kIkkmpXU
Rahotanni daga jami'ar UNIZIK dake kudancin Najeriya sun bayyana cewa, dalibai suk kai samame ofishin wani malamin jami'ar da suke zargi da nyman dalibai.
Saidai ko da ya hangosu suna zuwa, babu kaya a jikinsa haka ya fice daga ofishin nasa ta taga.
An hangi Bidiyon sa daliban na daika inda yake tserewa.
https://www.tiktok.com/@wisdom.ochie/video/7662895058336648469?_r=1&_t=ZS-985S5a82qKf
Ministan Ayyuka, David Umahi a karin farko yayi magana da 'yan jarida tun bayan rasuwar Mary Habila a gidansa.
Umahi Yace matashiyar ba mai aikin Tausa bace, kamar yanda aka rika yadawa, malamar Jinyace a Asibitin gwamnatin tarayya.
Yace kuma tana zaune a gidansa ne na shakatawa watau Guest House ita da wata, yace shskararta 3 a karkashinsa.
Yace kwana daya kamin rasuwarta, ta bayyanawa saurayinta cewa hancinta na zubar da Jyni.
Yace a ranar da zata rasu, sun yi waya da saurayinta da dare har tana ce masa bata so ya ajiye wayar amma ya ajiye, daga baya ya kirata, bata dauka ba.
Yace sai da aka balle dakin data rasu a ciki aka tarar da gawarta, sannan kuma an tarar da famfo na zuba, alamar tana shirin yin wanka ne.
Yace ya bayar da umarnin a yi bincike kan sanadin rasuwart...
Tauraruwar Tiktok daga jihar Sokoto wadda aka fi sani da Gorgeous wadda bata dake da fitowa daga kamen Hisbah ba inda tace ta tuba daga abubuwan da take aikatawa.
A yanzu ta sake sakin Bidiyoyi wanda suka daurewa mutane kai.
Da yawa dai sun bayyana cewa watau tuban muzuru ne ta yi.
https://www.tiktok.com/@gorgeous_ghurl/video/7662324827973291282?_r=1&_t=ZS-985Fz3kG8bx
Bayan da shahararriyar me wankin gidaje ta Abuja, Maryam Bulama ta bayyana cewa, Akwai wani Dan shekara 50 dake neman matar aure.
Sannan yana neman bazawara me shekaru 35 zuwa 40 ya aura duk me so ta bayyana kanta.
Da yawan mata zawarawa sun rika ajiye mata shekarunsu wasu ma da hotunansu suna cewa gasu.
Comment dinta ya cika da masu bayyana kansu inda suke cewa suna da bukatan hakan.
https://www.tiktok.com/@mbacleaningandlaundry/video/7662786025982397714?_r=1&_t=ZS-985E4ppiruj
Soja Boy yawa Malamin addinin islama, Sheikh Sani yahya Jingir rashin kunya ta hanyar Zhaghi.
Soja boy yayi wannan aika-aika ne a wata hira da aka yi dashi ta TiktokLive.
Ya zargi malam da karbar kudade a hannun 'yan siyasa yana cewa a zabi Tinubu.
https://www.tiktok.com/@hanyluv11/video/7662398018645232917?_r=1&_t=ZS-9859zEwJxH3
Hukumar 'yansandan Najeriya NPF ta sanar da sakamakon jarabawar daukar aikin mutane 50,000 aikin dansanda.
Me magana da yawun hukumar, PSC, Torty Njoku Kalu ne ya bayyana hakan ga manema labarai.
Yace wadanda suka rubuta jarabawar su duba shafin npfapplication.psc.gov.ng ranar Alhamis da misalin karfe 12 na dare dan ganin ko sun yi nasara.
An hangi matar dan takarar shugaban kasa na jam'iyyar NDC, Peter Obi nata tikar rawa.
Bidiyon ya jawo cece-kuce sosai inda wasu ke cewa tafi matar shugaban kasa, Bola Ahmad Tinubu komai wasu kuma na cewa basu yadda ba.
https://twitter.com/i/status/2077270145156714552