Friday, February 20
Shadow
Kalli Bidiyon: Ya Allah ina tawassuli da Azumin da na yi Allah kasa Pantami ba zai samu takarar gwamna da yake nema ba, Allah kasa ko Primary Election kada yaci>>Inji Dr. Hussain Kano

Kalli Bidiyon: Ya Allah ina tawassuli da Azumin da na yi Allah kasa Pantami ba zai samu takarar gwamna da yake nema ba, Allah kasa ko Primary Election kada yaci>>Inji Dr. Hussain Kano

Duk Labarai
Dr. Hussain Kano ya roki Allah da cewa kada ya baiwa Farfesa Isa Ali Pantami gwamnan jihar Gombe. A cewarsa, Farfesa Pantami ko da ya samu gwamnan jihar Gombe, zai jawowa Musulunci bacin sunane kawai dan ba mutumin kirki bane. Yace yana rokon Allah yasa kada Pantami yaci ko Primary Election. https://www.tiktok.com/@dr.hussainkano5/video/7609033520731737351?_r=1&_t=ZS-945Xbt6bHFJ
Da Duminsa: DSS sun sa ranar da zasu gurfanar da Malam Nasiru Ahmad El-Rufai a kotu

Da Duminsa: DSS sun sa ranar da zasu gurfanar da Malam Nasiru Ahmad El-Rufai a kotu

Duk Labarai
Rahotanni sun bayyana cewa, Hukumar 'yansandan farin kaya ta DSS ta saka ranar da zata gurfanar da tsohon Gwamnan jihar Kaduna, Malam Nasiru Ahmad El-Rufai a kotu. Rahoton yace DSS sun saka ranar 25 ga watan Fabrairu dan gurfanar da El-Rufai a gaban kotu. Za'a gurfanar dashine a gaban me shari'a, Joyce Abdulmalik bisa zargin kutse ma me baiwa shugaban kasa shawara kan harkar tsaro Malam Nuhu Ribadu a wayarsa.
Innalillahi  wa’inna ilaihi raji’un: Kalli Bidiyon Yanda wani ya karya Azuminsa, ranar 2 ga wata saboda an masa Alkawarin Naira Dubu 10 kacal

Innalillahi wa’inna ilaihi raji’un: Kalli Bidiyon Yanda wani ya karya Azuminsa, ranar 2 ga wata saboda an masa Alkawarin Naira Dubu 10 kacal

Duk Labarai
Wannan wani ne da aka nuna Bidiyon sa yana karya Azuminsa a ranar 2 ga watan Ramadana, watau Jiya kenan. A Bidiyon an ji wanda ya sashi ya karya Azumin na cewa zai bashi Dubu 10. Ya bashi Biskit da Ruwa yasha kuma ya ci. https://www.tiktok.com/@abuaffan46/video/7608644540722957588?_r=1&_t=ZS-944qkFfUMQT
Kalli Bidiyon: Yanda wata ‘yar Kudu ta nuna kayan abinci na tallafin Azumi da Gwamnatin tarayya ta aika mata

Kalli Bidiyon: Yanda wata ‘yar Kudu ta nuna kayan abinci na tallafin Azumi da Gwamnatin tarayya ta aika mata

Duk Labarai
Wannan wata 'yar kudu ce data nuna kalar tallafin kayan abinci na watan Ramadana da gwamnatin tarayya ta aika mata. Ta bude kwali inda ta rika zaro kayan abinci kala-kala dake ciki hadda rabin buhun shinkafa. Lamarin ya dauki hankula sosai. https://twitter.com/i/status/2024526037678248174 https://www.youtube.com/watch?v=wd0GSo07Ydo?si=qqRMJ9Ject5cILIv
Da Duminsa: Yayin da suke tsare dashi a Ofishinsu, ICPC sun kuma kai samame gidan Malam Nasiru Ahmad El-Rufai

Da Duminsa: Yayin da suke tsare dashi a Ofishinsu, ICPC sun kuma kai samame gidan Malam Nasiru Ahmad El-Rufai

Duk Labarai
Rahotanni sun bayyana cewa, ICPC sun kai samame a gidan tsohon Gwamnan jihar Kaduna, Malam Nasiru Ahmad El-Rufai. Sun kai samamenne a gidansa dake Aso Drive Abuja. Me magana da yawun Malam Nasiru Ahmad El-Rufai, Muyiwa Adekeye ne ya bayyana hakan a shafinsa na X. Ya kara da cewa, Lauyan Malam, Ubong Akpan yayi Allah wadai da wannan samamen inda yace take hakkin Malam ne da kuma yiwa harkar shari'a karan tsaye.
Innalillahi wa’inna ilaihi raji’un: Kalli Bidiyon yanda Hafsat Baby ta furta kalmar “Fita daga Musulunci ”  wajan cacar bakin da suke ita da Sadiya Haruna

Innalillahi wa’inna ilaihi raji’un: Kalli Bidiyon yanda Hafsat Baby ta furta kalmar “Fita daga Musulunci ” wajan cacar bakin da suke ita da Sadiya Haruna

Duk Labarai
Tauraruwar Tiktok, Hafsat Baby Ta Furta Kalmar Batanci ga Allah wadda malamai suka bayyana cewa tana kafurta duk wanda yayi. Hafsat ta Furta wannan mummunar kalmane a yayin da take Zhaghin Sadiya Haruna. Da yawa dai na ta mata raddi da gaya mata cewa ta fita daga Musulunci bata sani ba. https://www.tiktok.com/@king_malia1/video/7608428314855787796?_r=1&_t=ZS-943IBSOGojZ https://www.tiktok.com/@sayyada_sadiya_haruna/video/7607711602359471376?_r=1&u_code=ejaikd8elj8058&preview_pb=0&sharer_language=en&_d=ejaij098emc1h5&share_item_id=7607711602359471376&source=h5_m&timestamp=1771507497&user_id=7483197776647635989&sec_user_id=MS4wLjABAAAAN7fVbcc0mzRzgIxdVwTekj-Bzgfq381B8aILPWs15fqP6aFNZ5GwIpbLEwMTYvVW&item_author_type=2&social_share...
Allah Sarki Kalli Bidiyon: Malama Hafsat me Karatun Qur’ani a Tiktok ta koka bayan da Gwamna Abba Kabir Yusuf ya biya mata Umrah amma da sunayen wanda zasu tafi ya fito bata ga sunanta ba

Allah Sarki Kalli Bidiyon: Malama Hafsat me Karatun Qur’ani a Tiktok ta koka bayan da Gwamna Abba Kabir Yusuf ya biya mata Umrah amma da sunayen wanda zasu tafi ya fito bata ga sunanta ba

Duk Labarai
Tauraruwar Tiktok da ta shahara wajan Karatun Qur'ani da fadakarwa, Malam Hafsah ta koka da yanda Gwamnan Kanox Abba Kabir Yusuf ya biya mata Umrah amma da sunayen wadanda zasu tafi suka fito, bata ga sunanta ba. Ta yi Bidiyo a shafinta na Tiktok inda take kokawa da cewa 'yan uwa da abokan arziki duk sun san da zuwanta kuma ana ta mata fatan Alheri amma gashi yanzu suna ya fito babu sunanta. https://www.tiktok.com/@hafsatu_2/video/7608329873966255367?_r=1&_t=ZS-943Fdjp5DCz