Yariman Saudiyya Muhammad Bin Salman kenan aka gani yana wanke dakin ka'aba.
Da yawa sun jinjina masa saboda rashin girman kan da ya nuna.
https://twitter.com/i/status/2028391106790998205
A yayin da abubuwa ke kara kamari a gabas ta tsakiya.
Rahotanni na cewa, wata baraka ta kunno kai tsakanin kasar Saudiyya da kasar Amurka.
A wata hira da wakilin kasar Saudiyya yayi da Aljazeera, ya koka da cewa qasar Amurka, ta kwashe duk wasu makamanta daka iya tare hare-hare ta sama ta kaisu kasar Israyla.
Ya koka da cewa yayin da su kuma kasashen Larabawa da suka baiwa Amurkar Sansani ta ajiye sojojinta an barsu su ji da kansu.
Saidai Hukumar tsaro ta kasar Amurka tace suna tarewa kowace kasa barazanar harin da ake kai mata a yankin Larabawan.
Wani Bidiyo ya bayyana a kafafen sada zumunta inda aka ga jami'an tsaron kasar Saudiyya da yawa a dakin Ka'aba wanda ba'a saba ganin hakan ba.
Da yawa dai sun rika tabayar ko hakan na da alaka da matsalar tsaron dake faruwa ne ko kuwa wani abu ne na daban.
Bidiyon dai yasa mutane da yawa yin tambayoyi.
https://twitter.com/i/status/2028209339329368380
Wannan wata 'yar Najeriya ce dake kasar UAE inda tace ba zata dawo gida Najeriya ba duk abinda zai faru da ita saidai ya faru.
Ta bayyana hakane yayin da makaman kasar Iran ke ci gaba da zuba a kasar ta UAE.
https://twitter.com/i/status/2028247260853674194
Bidiyon Malam Nasiru Ahmad El-Rufai na jawabi ya bayyana.
Hakan na zuwane a karin farko tun bayan da ICPC da EFCC suka tsareshi bayan da ya amsa gayyatarsu.
Me magana da yawun Malam Nasiru ne ya wallafa Bidiyon jawabin nasa a shafinsa na X.
An jishi yana jawo hankalin mutane da su rungumi hanyar Lumana ta warware matsala, idan wata rashin jituwa ko wani abin damuwa ya samu, a kaiwa Hukuma, kamar yanda yace.
https://twitter.com/i/status/2028215253205467568
Saidai da Alama an dauki Bidiyon ne tun kamin ya shiga hannun EFCC amma sai yanzu aka sakeshi.
Wannan Bidiyon wasu matasa ne a jihar Kano da aka gansu a jikin gidan Gwamnatin jihar suna fadar cewa basa yin Tinubu, Najeriya sai Kwankwaso.
Anga Bidiyon yanda wani dan siyasa ya sha da kyar a hannun Matasan.
https://twitter.com/i/status/2028163419426136310
Rahotanni sun yi ta yawo a kafafen sada zumunta cewa, an kama me dafawa shugaban kasa, Bola Ahmad Tinubu abinci saboda zargin zubawa shugaban kasar Quba.
Saidai a martani ga wannan rahotan.
Fadar shugaban kasar ta bakin me magana da yawun shugaban kasa, Bayo Onanuga ya musanta wannan rahotan inda yace labarin kanzon Kurege ne.
https://twitter.com/i/status/2028147022314836130
Wasu rahotanni dake yawo a kafafen sada zumunta sun bayyana cewa, an kama me dafawa shugaban kasa, Bola Ahmad Tinubu abinci.
Rahotan dai na ta yawo inda mutane ke ta bayyana ra'ayoyisu akai.
Rahoton yace an kama me dafawa shugaban kasar abinci ne a asirce bayan zarginshi da sakawa shugaban kasar abinda bai dace ba cikin abinci.
Saidai zuwa yanzu fadar shugaban kasar bata ce komai akai ba.
https://twitter.com/i/status/2028045790053126279
An ga Tauraron fina-finan Hausa, Saheer Abdul tare da wata da aka bayyana cewa amaryarsa ce a Madina.
An ga yanda yake bata abinci a baki da yanda ya rike hannunta suke yawo a cikin massallaci.
Mutane sun musu sam barka inda akai ta musu fatan Alheri.
https://www.tiktok.com/@mr_saheeer/video/7611669650031512852?_r=1&_t=ZS-94JHBeNZla5