Saturday, February 14
Shadow
Kalli Bidiyon: Kashewa Iyalina Kudi yanzu na fara>>Inji Ahmad wanda ya kashe Naira Biliyan 1.5 ya hadawa ‘ya’yansa bikin Birthday a Kano

Kalli Bidiyon: Kashewa Iyalina Kudi yanzu na fara>>Inji Ahmad wanda ya kashe Naira Biliyan 1.5 ya hadawa ‘ya’yansa bikin Birthday a Kano

Duk Labarai
Ahmad wanda ya kashe makudan kudade wajan hadawa 'ya'yansa Bikin Birthday a Kano ya kawo Davido ya bayyana cewa kashewa Iyalinsa kudi yanzu ya fara. Ya bayyana cewa akwai mutane 100 da yakw shirin kaiwa Umrah a Azumin bana. Kuma yace surutun mutane be dameshi ba. https://www.tiktok.com/@our.lives/video/7606620274313792785?_r=1&_t=ZS-93uXYTebUzQ
Kalli Bidiyon: Duk da Hajiya Naja’atu ta cewa, Sheikh Pantami Maqaryaci amma Wallahi tafi malamai da yawa daraja a Idon Pantami>>Inji Dr. Hussain

Kalli Bidiyon: Duk da Hajiya Naja’atu ta cewa, Sheikh Pantami Maqaryaci amma Wallahi tafi malamai da yawa daraja a Idon Pantami>>Inji Dr. Hussain

Duk Labarai
Dr. Hussain Kano, dake fadakarwa a kafafen sada zumunta ya bayyana cewa, duk da zagin da Naja'atu tawa farfesa Isa Ali Pantami inda ta kirashi da maqaryaci, tafi malamai da yawa daraja a idonsa. Ya bayyana hakane a wani Bidiyonsa inda yake cewa da yanzu Naja'atu zata dawo tafiyar Pantami da gudu zai karbeta https://www.tiktok.com/@dr.hussainkano5/video/7606626853901651207?_r=1&_t=ZS-93uUz0CEfWT
Bafa ka fi karfin doka ba>>Gwamnatin Tarayya ta gayawa El-Rufai

Bafa ka fi karfin doka ba>>Gwamnatin Tarayya ta gayawa El-Rufai

Duk Labarai
Gwamnatin tarayya ta bayyanawa tsohon gwamnan jihar Kaduna, Malam Nasiru Ahmad El-Rufai cewa, bai fi karfin doka ba. Hakan ya fito ne daga bakin me magana da yawun shugaban kasa, Bayo Onanuga ta shafinsa na X inda yake martani kan kalaman El-Rufai na cewa, yana sauraren wayar da me baiwa shugaban kasa shawara akan harkar tsaro, Malam Nuhu Ribadu ke yi. ElRufai ya bayyana hakanne a hirar da aka yi dashi a Arise TV inda ya zargi Malam Nuhu Ribadu da bayar da umarnin a kamashi ta hanyar kiran waya ya bayar da umarni. ElRufai ya bugi kirjin cewa, suma suna sauraron hirarrakin wayar gwamnati. Onanuga yace hakan ba karamin laifi bane kuma ya kamata a binciki El-Rufai da 'yan koronsa, idan wannan ikirari nasa ya zama gaskiya a hukuntashi. https://twitter.com/i/status/202242392757...
Kalli Bidiyon: Awanni kadan bayan sakinta daga EFCC, Samha M. Inuwa ta bayyana cewa, babynta ya saya mata sabuwar mota

Kalli Bidiyon: Awanni kadan bayan sakinta daga EFCC, Samha M. Inuwa ta bayyana cewa, babynta ya saya mata sabuwar mota

Duk Labarai
Tauraruwar fina-finan Hausa, Samha M. Inuwa ta bayyana cewa,baby dinta ya sai mata sabuwar mota. Ta wallafa Bidiyon motar a shafinta na Tiktok. https://www.tiktok.com/@samha_m_inuwa/video/7606429500867448084?_r=1&_t=ZS-93tiKtYgDKK Hakan na zuwane awanni kadan bayan da EFCC suketa. Kotu dai ta yanke mata hukuncin daurin watanni 6 ko biyan tarar Naira 200,000.
Da Duminsa: ElRufai ya bayyana sunan wanda yasa DSS su kamashi

Da Duminsa: ElRufai ya bayyana sunan wanda yasa DSS su kamashi

Duk Labarai
Tsohon Gwamnan jihar Kaduna, Malam Nasiru Ahmad El-Rufai ya bayyana sunan malam Nuhu Ribadu me baiwa shugaban kasa shawara akan harkar tsaro da cewa shine yasa a kamashi. Ya bayyana hakane a hirar da aka yi dashi a gidan Talabijin na Arise TV inda yace kamar yanda gwamnati take sauraren kiraye-kirayen wayoyin mutane suma 'yan Adawa suna da hanyar sauraren kiraye-kirayen wayoyin Gwamnatin. ElRufai dai a baya yace Nuhu Ribadu mutuminsa ne amma daga baya ya canja.
Kalli Yanda aka bi Duk Zamfara aka lalata duk wata fasta ta shugaba Tinubu, Jam’iyyar APC tace abin ya isheta haka

Kalli Yanda aka bi Duk Zamfara aka lalata duk wata fasta ta shugaba Tinubu, Jam’iyyar APC tace abin ya isheta haka

Duk Labarai
Rahotanni daga jihar Zamfara na cewa wasu tsagera sun bi fastocin shugaban kasa, Bola Ahmad Tinubu sun lalatasu a fadin jihar. Sakataren yada labarai na jihar, Malam Yusuf Idris ne ya bayyana hakan a wata ganawa da manema labarai. Yace wannan cin fuskane wanda ba zasu yadda dashi ba inda yayi kira ga jami'an tsaro su dauki mataki kan lamarin.
Gwamnatin tarayya ta kasa bayar da umarnin Kotu na tsare malam Sheikh Khalifa Sani Zaria

Gwamnatin tarayya ta kasa bayar da umarnin Kotu na tsare malam Sheikh Khalifa Sani Zaria

Duk Labarai
A yayin da lauyan Malamin Addinin Islama, Sheikh Khalifa Sani Zaria da ake tsare dashi ake zargi da shiryawa shugaban kasa, Bola Ahmad Tinubu juyin Mulki ya shigar da kara kan a saki malamin. Mai shari'a Justice Peter Lifu ya bukaci lauyan Gwamnati daya kawo takardar kotu data bayar da damar a tsare malamin, saidai Lauyan Gwamnatin ya kasa kawo takardar inda yace a bashi lokaci. Mai shari'a Justice Peter Lifu ya bayyana bacin ransa sosai akan lamarin inda ya daga ci gaba da sauraren karar zuwa ranar Juma'a. An dai kama malam ne bisa zargin an aika masa Naira Miliyan 2 na aiki kan yiwa gwamnatin Tinubu juyin Mulki. Lauyan Malam, Sanusi Musa SAN ya shigar da karar EFCC, DIA, da babban lauyan Gwamnati, da kuma Bankin Ja'iz.