Friday, May 15
Shadow
Bidiyon mahajjata daga Jihar Adamawa suna kwana a waje a kasar Saudiyya ya dauki hankula

Bidiyon mahajjata daga Jihar Adamawa suna kwana a waje a kasar Saudiyya ya dauki hankula

Duk Labarai
Mahajjatan jihar Adamawa da suka je kasar Saudiyya sun rasa dakunan kwana inda aka gansu suna kwana a waje. Da yawa da aka yi hira dasu sun bayyana cewa basu da daki kuma suna neman hukumomin jiharsu dana kananan Hukumomin su amma basu gansu ba. An ji wanda ya dauki Bidiyon hana kokawa cewa ya kamata a dauki matakin da ya dace. https://twitter.com/i/status/2054860996850696454
Biyo bayan cewar da yayi ya samawa mutane aiki>>An zakulo tsohon Bidiyon Hon. Isa Ali Pantami inda yake cewa, A matsayinsa na Minista ba zai iya samarwa kowa aiki ba

Biyo bayan cewar da yayi ya samawa mutane aiki>>An zakulo tsohon Bidiyon Hon. Isa Ali Pantami inda yake cewa, A matsayinsa na Minista ba zai iya samarwa kowa aiki ba

Duk Labarai
A wata hira da Farfesa Hon. Sheikh Isa Ali Pantami yayi da gidan Talabijin na Trust TV ya bayyana cewa ya samarwa mutane aiki inda ake biyansu Albashi me tsoka Akwai zarge-zargen cewa, Farfesa Isa Ali Pantami bai samawa mutane da yawa ayyukan yi ba a matsayinsa na Minista lokacin mulkin tsohon shugaban kasa, Muhammadu Buhari. Saidai malam yace Ba yawan aikin bane, ingancin aikin ake bukata. Ya bayyana cewa,mutum daya daya kirashi yake masa godiya, yace masa aikin da ya samar masa ana biyansa Albashin Miliyan 80 a shekara. Saidai a yanzu kuma An zakulo wani tsohon Bidiyon malam innda yake cewa a matsayin sa na Minista, ba zai iya samarwa da kowa aiki ba. Hakane yasa wasu suka zargi malam da Tubka sa warwara. https://twitter.com/i/status/2054632543475896349
Karanta Jadawalin yawan mutanen dake dauke da cutar Kanjamau a kowace jihar Najeriya

Karanta Jadawalin yawan mutanen dake dauke da cutar Kanjamau a kowace jihar Najeriya

Duk Labarai
Wannan jadwalin mutanen dake karbar magungunan cutar Kanjamau ne a kowace jihar Najeriya. 1. Benue: 195,3052. ⁠Akwa Ibom: 158,2013. ⁠Lagos: 135,9184. ⁠Rivers: 90,0555. ⁠Nasarawa: 65,9966. ⁠FCT: 62,6277. ⁠Kaduna: 58,5768. ⁠Cross River: 57,7659. ⁠Enugu: 55,47810. ⁠Delta: 52,47511. ⁠Taraba: 51,84012. ⁠Abia: 50,03813. ⁠Imo: 47,86314. ⁠Plateau: 46,61815. ⁠Anambra: 46,60216. ⁠Adamawa: 42,07417. ⁠Kano: 41,09318. ⁠Kogi: 37,30119. ⁠Oyo: 33,13320. ⁠Niger: 33,05721. ⁠Ogun: 31,82222. ⁠Bauchi: 29,74523. ⁠Edo: 29,25624. ⁠Gombe: 28,03725. ⁠Osun: 25,01826. ⁠Borno: 24,52727. ⁠Ondo: 22,45528. ⁠Kebbi: 20,80329. ⁠Bayelsa: 19,54930. ⁠Katsina: 18,68231. ⁠Ebonyi: 15,47432. ⁠Kwara: 14,99733. ⁠Jigawa: 14,30234. ⁠Zamfara: 13,81335. ⁠Ekiti: 12,35636. ⁠Yobe: 10,71637. ⁠Sokoto: 10,511 Total: 1.70m...
Kalli Bidiyon: Matar tsohon Shugaban kasa, Muhammadu Buhari na rawa da ya dauki hankula

Kalli Bidiyon: Matar tsohon Shugaban kasa, Muhammadu Buhari na rawa da ya dauki hankula

Duk Labarai
Ganin Bidiyon matar tsohon shugaban kasa, Hajiya A'isha Buhari tana rawa ya dauki hankula a kafafen sada zumunta. A'isha Buhari ta yi rawar ne tare da wasu malaman Jinya mata inda suka yi amfani da wani salon wakar da ake yayi na jefa kyalle. Sun yi wannan ne dan murnar zagayowar ranar Malam Jinya ta Duniya https://twitter.com/i/status/2054300515463229822
Kalli Bidiyon da Duminsa: Tauraruwar Tiktok, Rahama Saidu(Me babban Shago) zata yi aure

Kalli Bidiyon da Duminsa: Tauraruwar Tiktok, Rahama Saidu(Me babban Shago) zata yi aure

Duk Labarai
Tauraruwar Tiktok, Rahama Saidu Me babban shago zata yi aure. Hakan ya bayyana ne bayan data wallafa wani Bidiyo inda aka ganta sanye da doguwar riga. A comment an ga wadanda suka santa suna ta tayata murna da fadin Allah ya kaimu ranar auren ita kuma tana ta amin. Saidai Bidiyon ya dauki hankula bayan da aka ga wani sabon zanen Tattoo da Rahama Saidu ta yi a gadon bayanta. https://www.tiktok.com/@rahamasaidu2/video/7638962049204129032?_r=1&_t=ZS-96IkIqZ8a2K A kwanakin baya dai, Rahama Saidu ta dauki hankula bayan da ta yi zanen Tattoo akan kirjinta. Saidai zuwa yanzu ba'a san wanene Rahama Saidun zata aura ba.
Kalli Bidiyon: Yanda Aka kama malamin Jami’a da dalibarsa a aji suna abinda bai kamata ba

Kalli Bidiyon: Yanda Aka kama malamin Jami’a da dalibarsa a aji suna abinda bai kamata ba

Duk Labarai
Dalibai a jami'ar Tansian University Oba, dake jihar Anambra aun kama Malami wanda kuma fasto ne da dalibarsa suna aikata abinda bai kamata ba a cikin Aji. An ga bidiyon yanda daliban suka kamo malamin suna yaga masa riga inda shi kuma yake shirin tserewa. Da yawa dai sun bayyana cewa da bai kamata a mai haka ba, kamata yayi a mikashi hannun hukuma. https://twitter.com/i/status/2054128560588103844 Aikata abinda bai kamata ba tsakanin dalibai da malamansu yakan faru a jami'o'i wanda hakan yana ciwa mutane musamman iyaye da shuwagabannin al'umma tuwo a kwarya.
Kalli Bidiyon: Kudi cike da Ghana Must Go ana rabawa mutane da hotunan Shugaba Tinubu akai da suka jawo cece-kuce

Kalli Bidiyon: Kudi cike da Ghana Must Go ana rabawa mutane da hotunan Shugaba Tinubu akai da suka jawo cece-kuce

Duk Labarai
An ga Bidiyon kudi cike da jakar Ghana Must Go a Anbulan me dauke da suna da hoton shugaban kasa, Bola Ahmad Tinubu ana rabawa mutane dan su sake zaben shugaban kasar. Masu rabon kudin na sanye da riguna masu dauke da tamburan shugaba Tinubu kuma an jisu suna yarbanci. https://twitter.com/i/status/2053940653847966089 Ko da a shekarar 2023 ma an ga irin wanan yanda aka rika rabawa mutane kudi a Ghana Must Go dan su zabi shugaban kasar. A wancan lokacin har motar kudi irin ta banki aka ga ta shiga gidan na Tinubu dake Lagos. A wasu rahotannin daga baya bayan ya ci zabe, sun ce shugaba Tinubu ya rika bayyana cewa kudinsa suka bashi damar zama shugaban kasa.