Friday, April 10
Shadow
Yanda aka shirya munafurcin Tsigeni a matsayin Gwamna da hadin Bakin Mataimakina, Gwarzo, dan ya gajeni>>Inji Gwamnan Kano, Abba Kabir Yusuf

Yanda aka shirya munafurcin Tsigeni a matsayin Gwamna da hadin Bakin Mataimakina, Gwarzo, dan ya gajeni>>Inji Gwamnan Kano, Abba Kabir Yusuf

Duk Labarai
Gwamnan jihar Kano, Abba Kabir Yusuf ya bayar da labarin yanda aka shirya munafurcin tsigeshi a matsayin Gwamna tare da hadin gwiwar mataimakinsa da ya sauka, Gwarzo. Gwamnan yace an shirya tsigeshi ne sai kuma Gwarzo ya maye gurbinsa. Yace amma sai Allah bai basu nasara ba. Gwamnan ya bayyana hakane a yayin ganawa da wasu magoya bayansa. Yace yaji ance mataimakin nasa ya sauka daga mukaminsa amma har yanzu shi bai ga takardar ajiye aikin nasa ba.
Kalli Bidiyon: Akwai sanda bani da ko sisi a Asusun bankina kawai sai na tuna ashe ina da karama, sai nayi addu’a, Dubu dari biyar ta shiga Asusun bankina>>Inji Fasto

Kalli Bidiyon: Akwai sanda bani da ko sisi a Asusun bankina kawai sai na tuna ashe ina da karama, sai nayi addu’a, Dubu dari biyar ta shiga Asusun bankina>>Inji Fasto

Duk Labarai
Wani fasto ya bayyana yanda a cewarsa yayi wata addu'a a yayin da bashi da ko sisi sai ga Naira 500,000 a asusun bankinsa. Faston ya gayawa mabiyansa hakane a cocinsa inda yace idan mutum na da karfin Imani da karama, zai iya sarrafa Dukiyar Duniya. https://twitter.com/i/status/2042277160753209568
Kalli Bidiyon: A karshe dai Gwamnan Kano, Abba Kabir Yusuf ya fito da kansa ya bayyana dalilin ficewa daga NNPP zuwa APC

Kalli Bidiyon: A karshe dai Gwamnan Kano, Abba Kabir Yusuf ya fito da kansa ya bayyana dalilin ficewa daga NNPP zuwa APC

Duk Labarai
Gwamnan jihar Kano, Abba Kabir Yusuf ya fito yake bayyana dalilin ficewarsa daga jam'iyyar NNPP zuwa APC. Gwamna Abba ya bayyana cewa, wun hango wani katon dutsene suka ce a kauce a bi hanya amma aka kiya. Gwamnan yace shiyasa su suka nemawa kansu Mafita. https://twitter.com/i/status/2042502762395476427 https://twitter.com/i/status/2042381103663636501
Kalli Bidiyon: Yanda Dr. Hussain Kano ya hada hotonsa da fati Nijar ta dora hannu akan kirjinsa

Kalli Bidiyon: Yanda Dr. Hussain Kano ya hada hotonsa da fati Nijar ta dora hannu akan kirjinsa

Duk Labarai
Tauraron me fadakarwa a kafafen sada zumunta, Dr. Hussain Kano wanda a baya ya sha sukar 'yan fim, amma yanzu ya kamu da soyayyar mawakiya, Fati Nijar yayi wani hadin hoto da Fatin wanda ya dauki hankula. An ga hoton da ya hada, Fati ta dora hannu akan kirjinsa. Sannan an ga wani Bidiyon da ya wallafa yana fadin cewa, akan Fati zai iya batawa da kowa. https://www.tiktok.com/@dr.hussainkano5/video/7626949314488732946?_r=1&_t=ZS-95Pr9GDvD8L&sp_source=7537614245375297080
Kalli Bidiyon yanda Shuwagabannin kananan hukumomi a jihar Jigawa ke rokon Gwamnan jihar bayan ya kulle musu asusun bankunansu

Kalli Bidiyon yanda Shuwagabannin kananan hukumomi a jihar Jigawa ke rokon Gwamnan jihar bayan ya kulle musu asusun bankunansu

Duk Labarai
Rahotanni daga jihar Jigawa na cewa, Gwamnan jihar ya kulle asusun kananan hukumomin jihar har na tsawon watanni 3 bayan da ya gano suna Almubazzaranci da dukiyar al'umma. Gwamnan ya dauki wannan matakinne bayan gano cewa wasu daga cikin shuwagabannin kananan hukumomin na ware Naira Miliyan 70 dan yin Adashi. https://twitter.com/i/status/2042000355043516418