Da Duminsa: Da gaskene mun fara karbar Harajin saka Solar a gidaje>>Gwamnati ta tabbatar
A jiyane Bidiyo ya yadu sosai bayan da aka ga wani mutum a Legas yana ta fada da jami'an Gwamnati da suka je karbar harajin saka solar da yayi a gidansa.
Mutumin dai yace ba zai biya ba.
Inda mutane da yawa suka goyi bayansa.
Bidiyon ya jawo cece-kuce sosai inda mutane sukai ta bayyana cewa ko da sune ba zasu yadda ba.
A martanin Gwamnatin jihar Legas ta bakin me magana da yawun Gwamnan jihar, Wale Ajetunmobi ya bayyana cewa da gaskene akwai harajin sala sola a gida.
Yace amma ba ga duka mutanen jihar Legas ba, ana karbar Harajinne kawai a hannun wadanda suke a gidajen Gwamnatin jihar.








