Sunday, April 12
Shadow
Maimakon Zagina, A samu wani yayi taimakon Musulunci ya aureni>>Inji Hafsee

Maimakon Zagina, A samu wani yayi taimakon Musulunci ya aureni>>Inji Hafsee

Duk Labarai
Tauraruwar Tiktok me amfani da sunan Hafseey ta bayyana cewa a daina Zaginta. Tace maimakon zagin da ake mata, me zai hana a samu wani yayi taimakon Musulunci ya aureta? Ta bayyana hakane a shafin nata na Tiktok inda tace duk wanda yasan da gaske yake kuma yana da sana'a ya fito ya mata magana da DM. https://www.tiktok.com/@hafseeyyarmalam1/video/7627408585479245077?_r=1&_t=ZS-95U0PZLKaaf
Da Duminsa: Ganduje da Doguwa sun bayyana wanda suke son a baiwa mataimakin gwamnan jihar Kano

Da Duminsa: Ganduje da Doguwa sun bayyana wanda suke son a baiwa mataimakin gwamnan jihar Kano

Duk Labarai
Dan majalisar Wakilai, Alhassan Ado Doguwa da Tsohon shugaban jam'iyyar APC, Dr. Abdullahi Umar Ganduje sun bayyana wanda suke so a baiwa Mataimakin Gwamnan jihar Kano. Duka su biyun sun bayyana Murtala Garo a matsayin wanda suke son a baiwa mataimakin Gwamnan jihar ta Kano. Doguwa ya bayyana hakane a wata sanarwa da ya fitar ranar Lahadi a Abuja. Rahoton yace an cimma matsayar a zabi garo a matsayin mataimakin Gwamnan jihar Kano ne bayan wani zama da masu fada aji na jam'iyyar APC a jihar Kano suka yi ranar Asabar. Kuma kaso 90 cikin 100 na mutanen suka ce sun amince a zabi Garo a matsayin mataimakin gwamnan jihar.
Da Duminsa: Kun dai san ni Sanata ne koh? Toh wallahi tunda Tinubu ya zama shugaban kasa, babu kasafin kudin da aka aiwatar sacw kudin kawai suke>>Inji Sanata Aminu Waziri Tambuwal

Da Duminsa: Kun dai san ni Sanata ne koh? Toh wallahi tunda Tinubu ya zama shugaban kasa, babu kasafin kudin da aka aiwatar sacw kudin kawai suke>>Inji Sanata Aminu Waziri Tambuwal

Duk Labarai
Sanata Aminu Waziri Tambuwal tsohon Gwamnan jihar Sokoto ya bayyana cewa, kasafin kudin shekarar 2023, dana 2024 dana 2025 duk ba'a aiwatar dasu ba. Yace Sace kudin kawai suke. Ya bayyana hakane a kan wani dandamali inda yake wa jama'a jawabi. Bidiyon jawabin nasa ya watsu sosai a kafafen sada zumunta. https://twitter.com/i/status/2043350800794079279
Kalli Bidiyon: Yanda wata Uwar Ango daga Arewa ta baiwa Amarya kyautar Fan Miliyan 10, kwatankwacin Naira Biliyan 25 kenan a matsayin Budan kai

Kalli Bidiyon: Yanda wata Uwar Ango daga Arewa ta baiwa Amarya kyautar Fan Miliyan 10, kwatankwacin Naira Biliyan 25 kenan a matsayin Budan kai

Duk Labarai
Wannan Bidiyon ya dauki hankula a kafafen sada zumunta sosai inda aka ga mahaifiyar Ango daga Arewa ta baiwa Amarya Fan Miliyan 10, kwatankwacin Naira Biliyan 25 kenan. Lamarin ya dauki hankula kuma ya jawo cece-kuce inda ake ta bayyana mamaki da faruwar hakan. Wasu kuma sun ce hakan Almubazzaranci ne. https://twitter.com/i/status/2043223867833942266
Kalli Bidiyon: Ban taba samun matsala da matata ba saboda fim koda kuwa ta gannu ina soyayya a fim>>Inji Ali Nuhu

Kalli Bidiyon: Ban taba samun matsala da matata ba saboda fim koda kuwa ta gannu ina soyayya a fim>>Inji Ali Nuhu

Duk Labarai
Tauraron fina-finan Hausa, Ali Nuhu ya bayyana cewa bai taba samun matsala da matarsa ba game da harkar fim ko da ta ganshi yana soyayya da wasu mata a fim ba. Ali Nuhu yace, dalili shine yana girmama matar tashi kuma itama tana girmamashi sannan kuma wani lokacin ma yana bata labarin fim din ta karanta. https://twitter.com/i/status/2043028977996996987
Kalli Bidiyon: Aure nake so kuma wallahi ba da wasa nake ba, duk me sona da gaske yamin magana>>Inji Fatima

Kalli Bidiyon: Aure nake so kuma wallahi ba da wasa nake ba, duk me sona da gaske yamin magana>>Inji Fatima

Duk Labarai
Tauraruwar Tiktok me suna Fatima ta bayyana cewa aure take son yi. Ta bayyana hakane a shafinta ta Tiktok a Bidiyon guda biyu data yi inda a na farko tace aure take so. Daga baya kuma ta sake fitowa ta jaddada bukatarta. Tace duk me sonta ya mata DM, inda ta kara da cewa, a garin Kaduna take. https://www.tiktok.com/@khadeejamuhammed8/video/7627679047144705300?_r=1&_t=ZS-95TIWzXn8fQ
DSS na binciken hadiman Gwamnan Kano, Abba Kabir Yusuf guda 5 saboda zargin batawa Kwankwaso suna

DSS na binciken hadiman Gwamnan Kano, Abba Kabir Yusuf guda 5 saboda zargin batawa Kwankwaso suna

Duk Labarai
Hukumar 'yansandan farin kaya ta DSS na binciken Hadiman gwamnan Kano, Abba Kabir Yusuf su 5 bayan korafin da tsohon Gwamnan jihar, Dr. Rabiu Musa Kwankwaso ya shigar inda yake zarginsu da bata masa suna. Wadanda aka kama din sune me taimakawa Gwamna Abba ta bangaren kafafen sadarwa, Sanusi Bature, Dawakin Tofa, da shugaban matasa na APC, Salisu Yahya Hotoro, sai Ibrahim Adam wanda shine ke baiwa Gwamna Abba Shawara kan yada labarai sannan tsohon Hadimin Kwankwaso ne, Sai Nuhu Dambazau da Mukhtar S. Yahuza. Rahoton yace dukansu da kansu suka kai kansu ofishin DSS bayan gayyatar da aka musu. Kwankwaso ne da kansa ya sakawa takardar korafin hannu inda ya zargesu da ci masa mutunci da bata masa suna a kafafen sada zumunta.
Bayan da aka shafe kwana da kwanaki ana neman matar auren nan, a karshe dai an iske ta a dakin Otal ita da Qartonta suna shakatawa

Bayan da aka shafe kwana da kwanaki ana neman matar auren nan, a karshe dai an iske ta a dakin Otal ita da Qartonta suna shakatawa

Duk Labarai
Wata matar aure me suna Mrs Tilewa Olatunde Funke 'yar kimanin shekaru 42 ta bace ana ta nemanta. Lamarin ya farune a garin Ilara-Mokin na jihar Ondo. Saidai da bincike ya tsananta, 'yan sanda sun ganota a dakin otal da wani me suna Isa Alaba dan kimanin shekaru 55 a dakin otal suna shakatawa. Hukumar 'Yansandan ta bayyana cewa matar da kanta ta kai kanta wajan mutumin ba garkuwa yayi da ita ba kuma an warware matsalar cikin ruwan sanyi. Hukumar 'Yansandan ta yi kira ga mutane dasu daina yada labaran da basu inganta ba kan lamarin.
Da Duminsa: Sabon rikici ya kunno kai a jam’iyyar ADC inda wani babban mutum shima ya maka su David Mark da Aregbesola a kotu yace ba halastattun shugabannin jam’iyyar bane

Da Duminsa: Sabon rikici ya kunno kai a jam’iyyar ADC inda wani babban mutum shima ya maka su David Mark da Aregbesola a kotu yace ba halastattun shugabannin jam’iyyar bane

Duk Labarai
Dan majalisar wakilai, Leke Abejide wanda dan jam'iyyar ADC ne ya maka shuwagabannin jam'iyyar na riko David Mark, da Rauf Aregbesola a kotu inda yace kotu ta saukesu. Hakan na zuwane a yayin da ake tsaka da fama da rikicin Nafiu Bala. Ya shigar da karar ne a gaban babbar kotun tarayya dake Abuja inda kotun ta tsayar da ranar 13 ga watan Afrilu dan yanke hukunci. Jam'iyyar ADC na fuskantar kalubale kala-kala inda take zargin hannun APC a lamarin.