Saturday, May 9
Shadow
Da Duminsa: An samu Wani me rufin Asiri da yace zai auri Zulaihat

Da Duminsa: An samu Wani me rufin Asiri da yace zai auri Zulaihat

Duk Labarai
" Idan Har Iyayen Aisha Zasu Bani Ita Wallahi Zan Biya Mata Kudin Zuwa Saudiya Taje Dakin Ka'abah Ta Fara Addu'oin Neman Gafara Ga Allah, Bayan Ta Dawo Zan Aureta Tareda Nema Mata Makaranta Domin Ta Cigaba Da Karatu Cewar, Matashin Dan Kasuwa Daga Jihar Sokoto Mudassir Umar Abba Dun Allah ku taimaka min da (sharing) domin sakon ya isa inda ya kamata Allah yasaka da alheri 🤲🤲🙏✅
Kalli Bidiyon yanda Dansandan Najeriya yayi Mankas da giya yana ta tambele

Kalli Bidiyon yanda Dansandan Najeriya yayi Mankas da giya yana ta tambele

Duk Labarai
Wannan Bidiyon wani dansandan Najeriya ne da aka ga yayi mankas da giya yana ta tambele yana rungumar benci. Lamarin ya farune a garin Asin dake karamar hukumar Ikole Local a jihar Ekiti. Jama'ar gari da suka lura da abinda ke faruwa dashi, sun matsa kusa dashi dan taimaka masa. https://twitter.com/i/status/2052874591693840858 Da yawa dai na kira ga hukumar 'yansandan da ta yi bincike akansa.
A karin farko, Zulaihat wadda Saurayinta yawa Tonon Silili ta fito ta yi magana

A karin farko, Zulaihat wadda Saurayinta yawa Tonon Silili ta fito ta yi magana

Duk Labarai
Matashiya Zulaihat wadda saurayinta yawa tonon silili Bidiyon a ya rika yawo a kafafen sada zumunta a karin farko ta fito ta yi magana Abinda tace shine, An ji a wani Bidiyo dake ta yawo a kafafen sada zumunta kamar ta kira saurayin da ya mata wannan abu tana gaya masa cewa, Allah ya isa. Sannan kuma tace masa bata yafe abinda ya mata ba inda ta sha Alwashin ramawa. Saidai da yawa suna bata shawarar ta kyaleshi kawai ta mika lamarinta ga Allah. .
Karfin Hali:Kalli Yanda ‘yan Iskan Lagos sua tsare wata mota data lalace akan hanya suka ce sai an basu dubu 50 zasu bar motar ta wuce

Karfin Hali:Kalli Yanda ‘yan Iskan Lagos sua tsare wata mota data lalace akan hanya suka ce sai an basu dubu 50 zasu bar motar ta wuce

Duk Labarai
Bidiyon 'yan iskan Lagos ya bayyana a kafafen sada zumunta inda aka gansu sun hana wata babbar mota data lalace a gefen hanya wucewa wai sai an basu dubu 50. An ga wani soja ya je ya samesu yana musu magana, saidai sun gayawa sojan idan yana son su bar wajan to ya basu dubu 50 din da suke nema. https://twitter.com/i/status/2052465276185374721
Farashin Dala a kasuwar Chanji ta yau, Juma’a

Farashin Dala a kasuwar Chanji ta yau, Juma’a

Duk Labarai
Farashin dala a kasuwar Chanji ta Gwamnati a yau, Juma'a, 8 ga watan Mayu na shekarar 2026 ya kamane akan Naira ₦1,366 kan kowace dala. Bayan da gari ya waye, Farashin ya dan motsa inda ya rika hawa yana sauka tsakanin Naira ₦1,362 zuwa Naira ₦1,370 A kasuwar bayan fage kuwa, ana sayen dalar akan Naira ₦1,385 inda ake sayar da ita kan Naira ₦1,395 zuwa Naira ₦1,400 akan kowace dala.
Kalli Bidiyon: Wannan matashiyar ta yi bayani dalla-dalla yanda ‘yan mata zasu rika kiyayewa kada saurayi ya daukesu Bidiyo idan suka je Otal

Kalli Bidiyon: Wannan matashiyar ta yi bayani dalla-dalla yanda ‘yan mata zasu rika kiyayewa kada saurayi ya daukesu Bidiyo idan suka je Otal

Duk Labarai
Wannan matashiyar me suna Auta, ta baiwa mata shawarar yanda zasu rika kiyayewa kada namiji ya daukesu Bidiyo idan sun je Otal. Ta bayyana cewa, Ana saka kyamara a harshe a kunne, da haba da sauransu dan haka mata su kiyaye kada a daukesu Bidiyo. https://www.tiktok.com/@autahmadaki/video/7637058301036940564?_r=1&_t=ZS-96BRtcpeHYW
Kalli Bidiyon: Masoyan Adam A. Zango sun ce zasu sai mata fom din takarar Gwamna ko sanata a Kaduna

Kalli Bidiyon: Masoyan Adam A. Zango sun ce zasu sai mata fom din takarar Gwamna ko sanata a Kaduna

Duk Labarai
Masoyan Tauraron fina-finan Hausa, Adam A. Zango sun sha Alwashin sai masa fom din takarar gwamna ko dan majalisa a jihar Kaduna. Sun kuma sha alwashin tsayawa dan yi masa yakin neman zabe. Saidai a martaninsa, Adam A. Zango yace shi yana tare da mataimakin shugaban kasa, Kashim Shettima amma ya gode da soyayyar da masoyan nasa suka nuna masa. https://www.tiktok.com/@og_adam_a_zango_official/video/7637211514897829140?_r=1&_t=ZS-96BRNTllfQ8
Allah Sarki: Kalli Bidiyon yanda mahaifiyar ta taje gidan su matashin da yawa ‘yarta tonon silili amma mahaifansa suka koreta

Allah Sarki: Kalli Bidiyon yanda mahaifiyar ta taje gidan su matashin da yawa ‘yarta tonon silili amma mahaifansa suka koreta

Duk Labarai
Bidiyon ya bayyana dauke da muryar wadda ake cewa, itace mahaifiyar matashiya Halima wadda Bidiyon ta ya karade kafafen sada zumunta. An ji Mahaifiyar tata na bayar da labarin yanda ta samu labarin abinda ya faru da diyarta kuma har ta je gidan su yaron da yawa diyar tata tonon silili. Tace ta hadu da mahaifiyar yaron da mahaifinsa inda suka tattauna a karshe dai mahaifinsa yace mata tunda ba ciki yawa diyarta ba kawai kowa yayi hakuri a karshe yace ta tashi ta fitar musu daga gida. https://www.tiktok.com/@kontogwange/photo/7637175943211027720?_r=1&_t=ZS-96BQYBCvVlQ Da yawa dai sun rika bayyana cewa gadukkan Lamu mahaifin yarinyar bashi da rai. Danna nan dan kallon Bidiyon https://www.tiktok.com/@kontogwange/photo/7637175943211027720?_r=1&_t=ZS-96BQYBCvVlQ