Saturday, April 4
Shadow
Nafiu Bala wanda ya kai Su Atiku, El-Rufai, Kwankwaso, Peter Obi Kotu yace shine shugaban APC amma suna son yi masa kwace, ya aikawa kasar Amurka Takardar korafi

Nafiu Bala wanda ya kai Su Atiku, El-Rufai, Kwankwaso, Peter Obi Kotu yace shine shugaban APC amma suna son yi masa kwace, ya aikawa kasar Amurka Takardar korafi

Duk Labarai
Nafiu Bala Gombe wanda ke ikirarin shine shugaban jam'iyyar ADC kuma ya maka su Atiku, El-Rufai, Kwankwaso, da Peter Obi a kotu yace suna son rabashi da mukaminsa ta hanyar karfa-karfa ya aikawa kasar Amurka da korafi. Nafiu ya ce a cikin takardar a dokar jam'iyyar ADC, idan shugaba ya sauka mataimakinsa ne ke karbar shugabancin jam'iyyar, yace dan haka da tsohon shugaban jam'iyyar ya sauka, Shine halastaccen shugaba. Saidai yace su Atiku, El-Rufai, Kwankwaso, da Peter Obi sun je sun masa karfa-karfa. Yace suna zargin wai shugaban kasa ne ko jam'iyyar shugaban kasa ce ta dauki nauyinsa amma yace ba gaskiya bane bashi da alaka da APC ko shugaban kasa. Yace dan haka yana kira ga kasar Amurka data hana wadannan mutane shiga kasarta.
Kalli Bidiyon: Idan na ci gaba da magana ba zamu iya barin garinnan ba kuma ba ku da inda zamu iya kwana>>Shugaba Tinubu ya gayawa al’ummar Jos inda ya yanke maganar da yake

Kalli Bidiyon: Idan na ci gaba da magana ba zamu iya barin garinnan ba kuma ba ku da inda zamu iya kwana>>Shugaba Tinubu ya gayawa al’ummar Jos inda ya yanke maganar da yake

Duk Labarai
A ziyarar da shugaban kasa, Bola Ahmad Tinubu ya kai jihar Filato an jiyoshi yana cewa babu lokaci, idan ya ci gaba da magana, ba lallai su iya komawa Abuja ba. Ya kara da cewa kuma a Jos babu inda zasu iya kwana, inda ya karkar maganarsa da wannan kalamai ya zauna. https://twitter.com/i/status/2040364555398787567 Wannan kalamai nasa dai sun jawo cece-kuce inda ake ganin basu dace ba. A baya dai shugaban yace garin Jos ba wutar lantarki inda yace kuma mintuna goma zasu yi su koma. Shugaban yaki shiga cikin garin Jos inda a filin jirgi ya tsaya saidai aka kai masa iyalan wadanda suka jikkata ya gana dasu a filin Jirgin. Hakan ya jawo masa suka sosai cikin wadanda suka sokeshi hadda tsohon Mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar. Saidai fadar shugaban kasa tace, shug...
Kalli Bidiyon: Kada wanda ya karya doka ko ya tayar da rigima saboda wani dan siyasa, Ba zaka ga yaran masu kudi irina muna haka ba>>Inji Hon Bello El-Rufai, dan tsohon Gwamnan Kaduna

Kalli Bidiyon: Kada wanda ya karya doka ko ya tayar da rigima saboda wani dan siyasa, Ba zaka ga yaran masu kudi irina muna haka ba>>Inji Hon Bello El-Rufai, dan tsohon Gwamnan Kaduna

Duk Labarai
Hon. Bello El-Rufai da a wajan tsohon Gwamnan Kaduna, Malam Nasiru Ahmad El-Rufai ya yi kira ga matasa kada su karya doka ko su tada rigima saboda wani dansiyasa. Yace ba zaka ga 'ya'yan masu kudi irinsa suna hakan ba. Wannan magana tasa ta jawo cece-kuce inda wasu suka goyi bayansa wasu kuma suka sokeshi. https://twitter.com/i/status/2040444856384844169
Wata Sabuwa: ‘Yan Jam’iyyar ADC sun fara barin jam’iyyar

Wata Sabuwa: ‘Yan Jam’iyyar ADC sun fara barin jam’iyyar

Duk Labarai
Rahotanni sun bayyana cewa 'yan Jam'iyyar ADC da yawane suka koma jam'iyyar NDC. Shugaban jam'iyyar, Seriake Dickson ne ya karbesu a gidansa dake Abuja. Tsohuwar 'yar ADC da jam'iyyar ta dakatar, Amanda Pam ce ta jagoranci 'yan jam'iyyar da yawa ciki hadda 'yan Kwankwasiyya reshen Abuja suka koma jam'iyyar ta NDC. Bayan su kuma akwai 'yan labour Party da 'yan SDP da suma suka koma jam'iyyar ta NDC. Daga cikinsu akwai dakataccen shugaban ADC na AMAC, Omale Sule, da shugabar mata ta ADC reshen Abuja, Princess Gladys Ngozi, tsohon shugaban jam'iyyar ADC na Kuje, Godwin Onoya, da tsohon mataimakin shugaban jam'iyyar ADC, Yusuf Adam da kuma tsohon shugaban matasa na jam'iyyar reshen Abuja, Aliyu Umar. Sauran sune tsohon shugaban jam'iyyar SDP reshen Abuja, Nurudeen Bissallah, da ...
Kalli Bidiyon yanda Shugaban kasa, Bola Ahmad Tinubu ya durkusa kasa ya gaishe da tsohon Shugaban kasa, Olusegun Obasanjo

Kalli Bidiyon yanda Shugaban kasa, Bola Ahmad Tinubu ya durkusa kasa ya gaishe da tsohon Shugaban kasa, Olusegun Obasanjo

Duk Labarai
Bidiyon yanda shugaban kasa, Bola Ahmad Tinubu ya durkusa kasa ya gaishe da tsohon shugaban kasa, Olusegun Obasanjo ya dauki hankula. Tinubu ya gaishe da Obasanjo ne a haka a yayin ziyarar da ya kai jihar Ogun. https://twitter.com/i/status/2040444550338973916 Wani abinda ya kara daukar hankulan mutane a ziyarar shine yanda aka ga gwamnonin Arewa sun raka shugaba Tinubu din jihar Ogun.
Kalli Bidiyon: An taba min Asiri saida na bar harkar Film Gaba daya, Ali Nuhu ne yasa akai ta saukar Qur’ani har na dawo>>Inji Fati Muhammad

Kalli Bidiyon: An taba min Asiri saida na bar harkar Film Gaba daya, Ali Nuhu ne yasa akai ta saukar Qur’ani har na dawo>>Inji Fati Muhammad

Duk Labarai
Tauraruwar fina-finan Hausa, Fati Muhammad ta bayyana cewa, an taba mata Kurciya har sai da ta bar harkar fim. Ta bayyana hakane a wata hira da Ali Jita yayi da ita. Ta bayyana cewa, Saida aka tsayar da kowane fim saida ta dawo sannan aka ci gaba. Tace Ali Nuhu ne ya sa aka rika sauke Qur'ani sai da ta dawo. https://www.tiktok.com/@ak.aiman2/video/7624919374545177863?_r=1&_t=ZS-95GHmaLoO3s&sp_source=7537614245375297080
Takarar Peter Obi a matsayin shugaban kasa, Kwankwaso ya maza mataimaki zata kayar da Tinubu Zabe inji dan gidan tsohon Gwamnan Kaduna, Bashir El-Rufai

Takarar Peter Obi a matsayin shugaban kasa, Kwankwaso ya maza mataimaki zata kayar da Tinubu Zabe inji dan gidan tsohon Gwamnan Kaduna, Bashir El-Rufai

Duk Labarai
Dan gidan tsohon Gwamnan Kaduna, Bashir El-Rufai ya bayyana cewa, tsayawa takarar Peter Obi a matsayin shugaban kasa, Kwankwaso yayi masa mataimaki ne zasu kayar da Shugaban kasa, Bola Ahmad Tinubu zabe. Ya bayyana hakane a X inda yace wannan hadi yana baiwa APC tsoro. https://twitter.com/i/status/2040382345325256781