Wednesday, February 25
Shadow
Da Duminsa: Kotu ta saurari karar da Malam Nasiru Ahmad El-Rufai ya shigar da ICPC da DSS a yau inda yake neman Jimullar Naira Biliyan 3

Da Duminsa: Kotu ta saurari karar da Malam Nasiru Ahmad El-Rufai ya shigar da ICPC da DSS a yau inda yake neman Jimullar Naira Biliyan 3

Duk Labarai
Rahotanni sun bayyana cewa, babbar kotun tarayya dake Abuja ta saurari karar da Malam Nasiru Ahmad El-Rufai ya shigar inda yake kalubalantar tsareshi da ake yi da kuma zarge-zargen da ake masa. Me magana da yawun Malam Nasiru, Muyiwa Adekeye ne ya bayyana hakan inda yace a yau, Kotun na sauraren karar take hakkin malam da ya shigar. Kotu taji duka bangarorin me kara da wanda ake kara inda ta daga karar zuwa ranar 27 ga watan February dan baiwa wanda ake karar damar tattara bayanai. https://twitter.com/i/status/2026602579300360622
Kalli Bidiyon: Yanda Sowore ya je hedikwatar ‘yansanda dan ya ga sabon IGP, Disu da shugaba Tinubu ya nasa, saidai ‘yansanda da yawa sun ce mas su basu ma san an nada sabon IGP ba

Kalli Bidiyon: Yanda Sowore ya je hedikwatar ‘yansanda dan ya ga sabon IGP, Disu da shugaba Tinubu ya nasa, saidai ‘yansanda da yawa sun ce mas su basu ma san an nada sabon IGP ba

Duk Labarai
Dan Fafutuka, Omoyele Sowore ya je Hedikwatar 'yansandan Najeriya dan ya ga sabon IGP saidai 'yansanda da yawa sun ce masa basu ma san an nada sabon IGP din ba. https://twitter.com/i/status/2026339895707312168 A cewarsu har yanzu Egbetokun ne yake akan kujerar.
Kalli Bidiyon: Gwamnan Kaduna ya baiwa malaman Addinin Islama da suka taimaka masa yaci zabe kyautar Tsabar Naira Miliyan 10

Kalli Bidiyon: Gwamnan Kaduna ya baiwa malaman Addinin Islama da suka taimaka masa yaci zabe kyautar Tsabar Naira Miliyan 10

Duk Labarai
Gwamnan jihar Kaduna, Malam Uba Sani ya baiwa Malaman Addinin Musulunci da suka taimaka masa yaci zabe a 2023 tsabar Naira Miliyan 10. Sannan yace a rabawa musu shinkafa kowannensu. Kwamishinan kananan Hukumomi na jihar, Sadiq Mamman Legas ne ya bayyana haka yayin da yake mika kyautar kudin. https://twitter.com/i/status/2026385771251601582
Innalillahi wa’inna ilaihi raji’un: A cikin Azumin Ramadana an kama wata Musulma da dadironta Kirista a Jihar Katsina

Innalillahi wa’inna ilaihi raji’un: A cikin Azumin Ramadana an kama wata Musulma da dadironta Kirista a Jihar Katsina

Duk Labarai
Rahotanni daga Dutsin Ma ta jihar Katsina na cewa, a cikin watan Azumin Ramadana, Hukumar Hisbah ta jihar ta kama wata mata me shekaru 26 tare da dadironta wanda Kirista ne me shekaru 35 a garin Dutsin ma. Rahoton yace an kamasu ne suna zaman dadiro a daki daya duk da ana cikin watan Ramadana. An kamata ne bisa jagorancin Hisbah karkashin shugabanta, Malam Shafi'u Ibrahim. Rahoton dai yace masoyan na zaunene ba tare da aure ba. https://twitter.com/i/status/2026229362165415980