Thursday, April 30
Shadow
Kalli Bidiyon: Musa Mai Sana’a ya yiwa Ali Jita zazzafan martani bayan da Ali Jita yayi magana akan tallata gwamnatin APC da yake yi

Kalli Bidiyon: Musa Mai Sana’a ya yiwa Ali Jita zazzafan martani bayan da Ali Jita yayi magana akan tallata gwamnatin APC da yake yi

Duk Labarai
Tauraron fina-finan Hausa, Musa Mai Sana'a yawa Ali Jita Zazzafan Martani kan maganar da yayi game da tallata Gwamnatin APC da yake yi. Ali Jita yace ya gayyaci Musa Mai Sana'a ya zo zauren tattaunawarsa dan ya amsa wasu tambayoyi game da tallata APC da yake yi amma bai je ba. Saidai a nasa maganar, Musa Mai Sana'a yace Ali Jita ya fita daga harkar rayuwarsa dan bai san yanda yake ciyar da iyalansa ba. Musa yace bai taba tambayar Ali Jita ba ya taimakeshi kuma shima da yace wasu 'yan siyasa suka bashi tallafi wa ya dameshi? https://www.tiktok.com/@maisanaakanotv/video/7634237707656498453?_r=1&_t=ZS-95xjDhJA6Rl
Kalli Bidiyon: Matashi ya tafi Abuja daga Kaduna a kasa dan zuwa jinjinawa shugaba Tinubu cewa aikinsa na kyau ba yunwa ba matsalar tsaro musamman a Arewa

Kalli Bidiyon: Matashi ya tafi Abuja daga Kaduna a kasa dan zuwa jinjinawa shugaba Tinubu cewa aikinsa na kyau ba yunwa ba matsalar tsaro musamman a Arewa

Duk Labarai
Wani matashi daga Kaduna, ya fara tattaki zuwa Abuja a kasa dan zuwa ya jinjinawa shugaban kasa, Bola Ahmad Tinubu kan kokarin da yake. Matashin yace babu yunwa babu matsalar tsaro a Arewa. Hakan na zuwane yayin da al'umma da yawa ke kukan cewa matsalar tsaro ta yi kamari musamman a yankin Arewa sannan kuma ga matsin rayuwa. https://www.tiktok.com/@agg_multimedia_services/video/7633896950009580818?_r=1&_t=ZS-95xiR4EWQIT
Jam’iyyar ADC ta bayyana matakin da zata dauka bayan da Kotu tace kada INEC ta yadda da sabbin shuwagabannin ta

Jam’iyyar ADC ta bayyana matakin da zata dauka bayan da Kotu tace kada INEC ta yadda da sabbin shuwagabannin ta

Duk Labarai
Jam'iyyar ADC reshen su David Mark, Atiku, Kwankwaso da sauransu, sun bayyana matakin da zasu dauka bayan da kotu tace kada INEC ta yadda da zaben da suka gudanar na zabar shuwagabannin su. A sanarwar daya fitar me magana da yawun jam'iyyar ADC, Bolaji Abdullahi ya bayyana cewa, zaben shuwagabannin da suka yi be soke shuwagabancin jam'iyyar a matakin jihohi ba. Inda suka ce shuwagabannin jihohi na jam'iyyar zasu ci gaba da shugaban cinsu har su kammala. Saidai Bolaji Abdullahi yace sun samu hukuncin kotun kuma zasu nemi lauyoyinsu su basu shawara kan abinda ya dace su yi.
Kai Duniya: Tauraruwar fina-finan Najeriya wadda matar aurece, ta gayyato kawarta mijinta ya biya bukatarsa dasu a lokaci guda

Kai Duniya: Tauraruwar fina-finan Najeriya wadda matar aurece, ta gayyato kawarta mijinta ya biya bukatarsa dasu a lokaci guda

Duk Labarai
Tauraruwar fina-finan kudancin Najeriya, Sisi Alagbado ta gayyatowa mijinta kawarta suka hadu a daki daya ya biya bukatarsa dasu. Wani ahin takaici shine sun dauki bidiyon kansu, kuma yanzu Bidiyon nata yawo a kafafen sada zumunta. Saidai bayan bayyanar Bidiyon, Sisi ta fito tana bayar da hakuri tana cewa, lallai itace da mijinta kuma sun aikata abin. Ta ce amma dan Allah masoyanta su yafe mata, tace ko abinci ta kasa ci.
Kalli Bidiyon: Wasu Akarammomi da sukace su masu kishin Arewa ne sun ce sun dukufa da saurakar Qur’ani ba dare ba rana har sai Allah ya baiwa Shugaba Tinubu nasarar cin zabe a karo na 2

Kalli Bidiyon: Wasu Akarammomi da sukace su masu kishin Arewa ne sun ce sun dukufa da saurakar Qur’ani ba dare ba rana har sai Allah ya baiwa Shugaba Tinubu nasarar cin zabe a karo na 2

Duk Labarai
Wadannan wasu alarammomi ne da suka bayyana cewa sun dukufa da saukar qur'ani ba dare ba rana har sai Allah ya baiwa shugaban kasa, Bola Ahmad Tinubu nasarar cin zabe a karo na biyu. Sun bayyana cewa suna wannan aiki ne saboda sun kasance 'yan kishin kasa ne. https://www.tiktok.com/@muhdusman247/video/7633883926385282325?_r=1&u_code=ejaikd8elj8058&preview_pb=0&sharer_language=en&_d=ejaij098emc1h5&share_item_id=7633883926385282325&source=h5_m&timestamp=1777452499&user_id=7483197776647635989&sec_user_id=MS4wLjABAAAAN7fVbcc0mzRzgIxdVwTekj-Bzgfq381B8aILPWs15fqP6aFNZ5GwIpbLEwMTYvVW&item_author_type=2&social_share_type=0&utm_source=copy&utm_campaign=client_share&utm_medium=android&share_iid=7625183675001341712&share_link_id=d...
Farashin Dala a kasuwar Chanji a yau, Laraba

Farashin Dala a kasuwar Chanji a yau, Laraba

Duk Labarai
, Farashin dala a kasuwar Chanji ta gwamnati a yau, Laraba 29 ga watan Afrilu na shekarar 2026 na akan Naira ₦1,360 kan kowace dala. Farashin ya dan motsa inda ya kai Naira ₦1,360.19 akan kowace dala, kamin daga baya ya dawo farashin sama. A kasuwar Bayan fage kuwa, farashin na dala ya kamane akan Naira ₦1,400 zuwa Naira ₦1,480 a kasuwannin Abuja, Kano, Lagos, da Fatakwal. Rahotanni sun ce a ranar Litinin data gabata, an sayar da dalar akan Naira 1390 a kasuwar ta bayan fage.
Wannan Bidiyon na shahararriyar me amfani da kafafen sada zumunta ya dauki hankula bayan da aka zargeta da aikawa mijin wata cewa sha’awa ta dameta yayi sauri ya zo wajanta

Wannan Bidiyon na shahararriyar me amfani da kafafen sada zumunta ya dauki hankula bayan da aka zargeta da aikawa mijin wata cewa sha’awa ta dameta yayi sauri ya zo wajanta

Duk Labarai
Kafar x ta cika da cece-kuce da tsokana da zunde bayan da wata shahararriyar me amfani da shafin me sunan @Firdaussyyyy ake zarginta da ta aikawa wani saurayinta wanda yana da mata cewa sha'awa take ji. Lamarin ya bayyana ne a yayin da cece-kuce ya barke tsakaninta da matar mutumin wanda tace ya saketa. Tace ta bar musu shi. Saidai Firdausi ta yi kokarin nuna cewa ba ruwanta da mijin matar Amma matar tace mata tana da sakon da ta aikawa mijin ta cewa tana jin sha'aw ya zo wajanta. Daga nan ne sai fiddausi ta yi shiru. https://twitter.com/i/status/2048835151044485557
Ana bari  Halas dan Kunya: Shiyasa na daina shan Giya>>Inji Tsohon Mataimakin shugaban kasa, Osinbajo

Ana bari Halas dan Kunya: Shiyasa na daina shan Giya>>Inji Tsohon Mataimakin shugaban kasa, Osinbajo

Duk Labarai
Tsohon Mataimakin shugaban kasa, Osinbajo ya bayyana cewa ya daina shan giyane saboda kunya duk da yasan cewa yasan giyar halas ce. Yace dalilin da yasa yake shan giya shine ya gani a baibul cewa Jesus ya mayar da ruwa giya. Yace dalilin da yasa ya daina sha shine, wata rana ya je yayi wa'azi a sansanin majalisar Dinkin Duniya dake Somalia ya kammala sai ya tafi wani gidan cin abinci dan ya sayi giya. Yace yana shiga sai ya tarar da mutane na ta shan giya amma suna ganinsa sai suka boye giyar, yace sai ya matsa kusa da wani yake tambayarsa me yasa suka boye giyar da suke sha? Sai yace ai shi malam ne basa son yaga suna shan giya. Yace daga nan yawa kansa fada yace duk da giyar ba halas bace amma ya daina sha.