Bidiyon tsohon Gwamnan jihar Sokoto, Dalhatu Bafarawa ya karade kafafen sada zumunta inda aka ganshi a wani yanayi.
Da yawa na cewa, yanzu an daina yayinsa.
https://twitter.com/SadeeqKurbe/status/2094069578418581577
Wannan wani mahaifine da ya dauki hankula a kafafen sada zumunta bayan da aka kamashi da matar dansa a dakin otal.
Dan ne da wasu abokansa suka je har dakin Otal din bayan da ya samu bayanan sirri cewa mahaifin nasa yana neman matar.
An ji Mahaifin yana bashi hakuri tare da fadin sharrin shedanne.
https://twitter.com/instablog9ja/status/2094111026539110904
Wani Mutum a jihar Sokoto ya dauki hankula bayan da ya fashe da kuka Biyo bayan zuwa Asibiti ya tarar Babu Likita.
An ganshi da marar Lafiyar da ya kai Asibitin yana ta kai da kawowa.
Da yawa dai sun yi Allah wadai da lamarin inda suka rika kira ga Gwamnatin Jihar data dauki mataki.
https://twitter.com/NigeriaStories/status/2094081236784341104
Matashiya Ajebo, Ta fito ta yi Allah ya isa akan Bidiyon ta dake yawo a kafafen sada zumunta.
A wani Bidiyo an jita tana ihu tana kuka tana cewa ba zata sake bin su Otega ba sannan ta daina zuwa Zoo road.
Bidiyon ya watsu sosai a kafafen sada zumunta inda me ake cewa ta je ta bi su Otega sun kwana a Otal ne shine 'yan uwanta suka bita suke mata hukuncin.
Saidai Ta fito ta karyata inda tace Bidiyon ta yi shine dan Nishadi.
Sannan tace duk wanda suka mata Muguwar fasara akan Bidiyon nata yafe musu ba.
https://www.tiktok.com/@ajebo784/video/7679444108250795285?_r=1&_t=ZS-99JfnDmPoKS
Amma me shafin Kwarmato na Mr. Unknown yace karya take 'yan gidansu ne suka mata hukunci a Bidiyon da aka ji tana ihu ba da wasa bane kamar yanda take ikirari.
https://www.tiktok.com/...
Wannan wani Dansanda ne dake ta shan Yabo a wajan jama'ar gari
'Yan Fhashi sun je sata inda 'yansanda suka tsere amma shi kadai ya tsaya ya shekye 'yan fashin 6 daya ya tsere ya je ya dawo da wasu.
Dansandan dai yana nan bai tafi ba, suma wanda suka dawo ya gama dasu.
Bayan gama Artabunne jama'ar gari suka je suna jinjina masa ana dagashi sama
https://www.tiktok.com/@officialmcjones_pixels/video/7678715081249017108?_r=1&_t=ZS-99JefOBOLpt
Wata Matashiya data yi karatun Qur'ani a shafinta na Tiktok ta dauki hankula sosai sabosa yin karatun ba daidai ba.
Da yawa na ce mata ta koma Islamiya inda tuni ta goge Bidiyon.
Saidai ta nuna bacin ranta da cewa dariyar da aka rika mata bata dace ba.
Ta bayyana cewa masu ce mata Jahila, Sune Jahilai dan ba wanda aka haifa da iyawa
https://www.tiktok.com/@salzee23/video/7679397686570667272?_r=1&_t=ZS-99JL5UEuERp
https://www.tiktok.com/@zee.baby070/video/7679484494713359636?_r=1&_t=ZS-99JLkESLXHQ
Taron malam Arewa 500 a Jihar Jigawa inda suka ce a sabi Shugaban kasa, Bola Ahmad Tinubu a 2027 ya jawo cece-kuce.
Wasu daga cikin malaman da suka halarci wajan sun fito sun barranta kansu da kalaman cewa wai a zabi Shugaban kasa, Bola Ahmad Tinubu a 2027 inda suka ce basu amince da hakan ba.
Wasu kuma suka yi zargin cewa yaudararsu aka yi zuwa wajan Taron.
Saidai a yanzu a samu wani Malami ya fito ya bayyana cewa kowane Malami an bashi Naira Miliyan 3 ne a wajan Taron.
https://twitter.com/MyksonDosSantos/status/2093729549938995291
Shugaban kasa, Bola Ahmad Tinubu ya baiwa kotun kasar Amurka Hujjoji 4 da yace ta yi la'akari dasu kada ta fitar da bayanan sirri dake kunshe da zargin da ake masa na safarar qaya.
Shugaban ya bayyana hakane ta hannun Lauyoyinsa Christopher Carmichael, Victor Henderson da Oluwole Afolabi.
Ya bayyana cewa babu dalilin da zai sa sai mutane sun san bayanan dake kunshe a cikin zargin da ake masa.
Sanan yace ana son a yi amfani da bayanan ne wajan cimma wani buri na siyasa.
Shugaban ya kuma ce dokar Amurka ta bashi kariya kan wannan bayanai tunda abune wanda ya shafeshi shi kadai dan haka sirrinsa ne.
Jam'iyyun Adawa da kungiyoyin fafutuka da yawa sun nemi a bayyana wadannan bayanai inda suke cewa 'yan Najeriya na da damar sanin irin rayuwar da shugaban kasar yayi a baya.
An kama Sojoji da suka yi Yunkurin yiwa shugaba kasar Nijar Juyin mulki.
Cikin sojojin da aka kama hadda mace.
Rahotanni sun bayyana cewa, Daga cikin sojojin Gwamnati ne aka samu baraka suka bar wajan sa aka turasu aiki suka afkawa fadar shugaban kasar dan kwace iko da mulkin kasar.
Sannan wasu daga cikinsu sun afkawa Filin sauka da tashi na jiragen saman kasar.
Saidai An dakile wannan yunkurin inda Rahotanni suk ce lamura sun dawo daidai a Jamhuriyar Nijar din.
https://twitter.com/KennedyWandera_/status/2093733601707737230
I
mam Khadi Badamasi Aliyu ya bayar da labarin wata matar aure da aka kaira Kabarinta wadda Kunamai suka mamaye kabarin.
Yace an yi ta addu'a amma kunaman suka ki gushewa.
Yace sai da aka kira Mijin matar aka ce ya yafe mata.
https://www.tiktok.com/@ag.islamic.tv1/video/7679169033849097493?_r=1&_t=ZS-99ID9rsvB4u