Mahaifiya data kai danta yayi Karatun Qur’ani, kammala amma bata raye
Allah Sarki, Labari me taba zuciya.
Wannan yaron mahaifiyarsa ta kaisa makarantar Haddar Qur'ani, ta mikashi hannun malamin tace duk abinda za'a masa a masa na ladaftarwa ita dai bayan shekara daya tana son ta ga ya zama mahaddacin Alqur'ani.
Malaminsa dake bayar da labarin Yace aka fara karatu.
Sai ta Kwanta jinya.
Malamin yace ya dauki dalibin me suna Isma'il Muhammad suka je duba mahaifiyar a Asibiti
Yace da suka je dubata, tana kwance a gadon Asibiti, ta rike hannun danta, tace abinda nake so da kai shine ka zama mahaddacin Qur'ani.
Yace bayan sun koma makaranta, ta sake kiran malamin tace wasiyyarta shine tana soj danta ya zama mahaddacin Qur'ani.
Amma yau gashi yaron ya haddace Qur'ani amma bata raye








