Friday, September 11
Shadow
Nasiru ya san matarsa tana kasar Morocco>>Inji Lauyan Khadija

Nasiru ya san matarsa tana kasar Morocco>>Inji Lauyan Khadija

Duk Labarai
Nasiru dake zargin Sheikh Dr. Ahmad Gumi da rike masa mata. Yasan cewa matarsa na kasar Morocco, idan yasan cewa tsakaninsa da matarsa suna zaman lafiya kamar yanda yake ikirari, to ya je ya dawo da ita. Sannan kudin sadakinta ma bai bata ba. Sannan akwai sanda suka yi fada, ya fitar da ita wajen gidan da suke da kayan bacci a jikinta ya kulle mata kofa ya hanata shiga gida Sannan ya gaya mata cewa ba zai saketa ko shekara dari za'a yi ana case, zai hana ta gaba ya hanata baya. Inji Lauyar Khadija Diab 'yar kasar Morocco me suna Bilkisu Abdulrasheed. https://www.tiktok.com/@rfi_ha/video/7684023040639896852?_r=1&u_code=ejaikd8elj8058&preview_pb=0&sharer_language=en&_d=ejaij098emc1h5&share_item_id=7684023040639896852&source=h5_m&timestamp=178911...
Gwamnatin tarayya zata fara baiwa dalibai data kyauta

Gwamnatin tarayya zata fara baiwa dalibai data kyauta

Duk Labarai
Gwamnatin tarayya ta bayyana cewa daga watan October me zuwa zata fara baiwa daliban Najeriya kyautar data ta 100MB. Ministan Ilimi, Tunji Alausa ne ya bayyana hakan a wata sanarwa ranar Alhamis. Ministan yace zasu hada kai da hukumar sadarwa ta kasa, NCC da tabbatar da wannan shiri nasu. Yace za'a fara da daliban sakandare dana jami'a ne kamin a fadada shirin daga baya. Yace sun dauki wannan matakine dan saukakawa daliban shiga shafukan kara Ilimi kyauta da kuma ragewa daliban radadin tsadar data.
Zan dorane daga inda shugaban kasa Bola Tinubu ya tsaya>>Inji Peter Obi

Zan dorane daga inda shugaban kasa Bola Tinubu ya tsaya>>Inji Peter Obi

Duk Labarai
Dan takarar shugaban kasa na jam'iyyar NDC, Peter Obi ya bayyana cewa idan ya zama shugaban kasa, zai ci gaba ne daga inda tsare-tsaren shugaban kasa, Bola Ahmad Tinubu daga inda ya tsaya. Yace dalili shine ba kowane abu da shugaba Tinubu yake yi bane kuskure. Yace kamar tsarin cire tallafin dala yace abune me kyau. Koda a baya ma dai Peter Obi yace idan ya zama shugaban kasa, ba zai dawo da tallafin man fetur ba zai ci gaba da ne akan tsarin shugaban kasa, Bola Ahmad Tinubu.
Kalli Bidiyon: Matar Shugaban kasa, Bola Ahmad Tinubu, Watau Remi tace bata taba zuwa jihar Zamfara ba

Kalli Bidiyon: Matar Shugaban kasa, Bola Ahmad Tinubu, Watau Remi tace bata taba zuwa jihar Zamfara ba

Duk Labarai
Matar shugaban kasa, Bola Ahmad Tinubu watau Remi tace ta zagaye jihohin Najeriya kaf amma banda jihar Zamfara. Ta bayyana hakane a jihar Imo yayin wani taron siyasa. Tace amma nan gaba tana son zata je jihar Zamfara inda ta karfafawa sauran mutanen Najeriya su rika zagayawa dan su san sauran 'yan uwansu 'yan Najeriya. Ta kuma bayyana cewa ita a makarantar sakandare, Abokanta na gaya mata cewa, tana kama da inyamurai. https://twitter.com/Imranmuhdz/status/2098105775633695139
Kalli Bidiyon: Yanda Mutanen jihar Zamfara suka rika fadin sai Atiku a yayin taron siyasa a gaban Gwamnan jihar Dauda Lawal Dare

Kalli Bidiyon: Yanda Mutanen jihar Zamfara suka rika fadin sai Atiku a yayin taron siyasa a gaban Gwamnan jihar Dauda Lawal Dare

Duk Labarai
Mutanen Jihar Zamfara sun rika fadin Najeriya sai Atiku a wajan yakin neman zaben shugaban kasa, Bola Ahmad Tinubu. Lamarin ya farune a gaban Gwamnan jihar na Zamfara, Dauda Lawal Dare. Bidiyon lamarin ya karade kafafen sada zumunta inda ake ta yadashi. https://twitter.com/emmaikumeh/status/2097944250625187933