Sunday, August 30
Shadow
Kalli Bidiyon: Wani da ya kai marar Lafiya Asibiti a Sokoto ya fashe da kuka bayan da ya tarar babu Likita

Kalli Bidiyon: Wani da ya kai marar Lafiya Asibiti a Sokoto ya fashe da kuka bayan da ya tarar babu Likita

Duk Labarai
Wani Mutum a jihar Sokoto ya dauki hankula bayan da ya fashe da kuka Biyo bayan zuwa Asibiti ya tarar Babu Likita. An ganshi da marar Lafiyar da ya kai Asibitin yana ta kai da kawowa. Da yawa dai sun yi Allah wadai da lamarin inda suka rika kira ga Gwamnatin Jihar data dauki mataki. https://twitter.com/NigeriaStories/status/2094081236784341104
Kalli Bidiyon: Matashiya Ajebo ta fito ta yi Allah ya isa kan Bidiyon ta dake yawo a kafafen sadarwa

Kalli Bidiyon: Matashiya Ajebo ta fito ta yi Allah ya isa kan Bidiyon ta dake yawo a kafafen sadarwa

Duk Labarai
Matashiya Ajebo, Ta fito ta yi Allah ya isa akan Bidiyon ta dake yawo a kafafen sada zumunta. A wani Bidiyo an jita tana ihu tana kuka tana cewa ba zata sake bin su Otega ba sannan ta daina zuwa Zoo road. Bidiyon ya watsu sosai a kafafen sada zumunta inda me ake cewa ta je ta bi su Otega sun kwana a Otal ne shine 'yan uwanta suka bita suke mata hukuncin. Saidai Ta fito ta karyata inda tace Bidiyon ta yi shine dan Nishadi. Sannan tace duk wanda suka mata Muguwar fasara akan Bidiyon nata yafe musu ba. https://www.tiktok.com/@ajebo784/video/7679444108250795285?_r=1&_t=ZS-99JfnDmPoKS Amma me shafin Kwarmato na Mr. Unknown yace karya take 'yan gidansu ne suka mata hukunci a Bidiyon da aka ji tana ihu ba da wasa bane kamar yanda take ikirari. https://www.tiktok.com/...

Kalli Bidiyon: Jarumin dansanda da ya kori ‘yan Fashi yana ta shan Yabo a wajan jama’ar gari

Duk Labarai
Wannan wani Dansanda ne dake ta shan Yabo a wajan jama'ar gari 'Yan Fhashi sun je sata inda 'yansanda suka tsere amma shi kadai ya tsaya ya shekye 'yan fashin 6 daya ya tsere ya je ya dawo da wasu. Dansandan dai yana nan bai tafi ba, suma wanda suka dawo ya gama dasu. Bayan gama Artabunne jama'ar gari suka je suna jinjina masa ana dagashi sama https://www.tiktok.com/@officialmcjones_pixels/video/7678715081249017108?_r=1&_t=ZS-99JefOBOLpt
Kalli Bidiyon: Matashiya ta dauki hankula a kafafen sada zumunta saboda yin Karatun Qur’ani ba daidai ba

Kalli Bidiyon: Matashiya ta dauki hankula a kafafen sada zumunta saboda yin Karatun Qur’ani ba daidai ba

Duk Labarai
Wata Matashiya data yi karatun Qur'ani a shafinta na Tiktok ta dauki hankula sosai sabosa yin karatun ba daidai ba. Da yawa na ce mata ta koma Islamiya inda tuni ta goge Bidiyon. Saidai ta nuna bacin ranta da cewa dariyar da aka rika mata bata dace ba. Ta bayyana cewa masu ce mata Jahila, Sune Jahilai dan ba wanda aka haifa da iyawa https://www.tiktok.com/@salzee23/video/7679397686570667272?_r=1&_t=ZS-99JL5UEuERp https://www.tiktok.com/@zee.baby070/video/7679484494713359636?_r=1&_t=ZS-99JLkESLXHQ
Kalli Bidiyon: A karshe dai an samu Malamin da ya bayyana nawa aka baiwa Malaman Arewa 500 da suka yi taro suka ce a zabi Tinubu a 2027

Kalli Bidiyon: A karshe dai an samu Malamin da ya bayyana nawa aka baiwa Malaman Arewa 500 da suka yi taro suka ce a zabi Tinubu a 2027

Duk Labarai
Taron malam Arewa 500 a Jihar Jigawa inda suka ce a sabi Shugaban kasa, Bola Ahmad Tinubu a 2027 ya jawo cece-kuce. Wasu daga cikin malaman da suka halarci wajan sun fito sun barranta kansu da kalaman cewa wai a zabi Shugaban kasa, Bola Ahmad Tinubu a 2027 inda suka ce basu amince da hakan ba. Wasu kuma suka yi zargin cewa yaudararsu aka yi zuwa wajan Taron. Saidai a yanzu a samu wani Malami ya fito ya bayyana cewa kowane Malami an bashi Naira Miliyan 3 ne a wajan Taron. https://twitter.com/MyksonDosSantos/status/2093729549938995291
Shugaba Tinubu ya baiwa Kotun Amurka hujjoji 4 da yace ta yi La’akari dasu kada ta fitar da bayanan dake kunshe da zargin safara Qaya da ake masa

Shugaba Tinubu ya baiwa Kotun Amurka hujjoji 4 da yace ta yi La’akari dasu kada ta fitar da bayanan dake kunshe da zargin safara Qaya da ake masa

Duk Labarai
Shugaban kasa, Bola Ahmad Tinubu ya baiwa kotun kasar Amurka Hujjoji 4 da yace ta yi la'akari dasu kada ta fitar da bayanan sirri dake kunshe da zargin da ake masa na safarar qaya. Shugaban ya bayyana hakane ta hannun Lauyoyinsa Christopher Carmichael, Victor Henderson da Oluwole Afolabi. Ya bayyana cewa babu dalilin da zai sa sai mutane sun san bayanan dake kunshe a cikin zargin da ake masa. Sanan yace ana son a yi amfani da bayanan ne wajan cimma wani buri na siyasa. Shugaban ya kuma ce dokar Amurka ta bashi kariya kan wannan bayanai tunda abune wanda ya shafeshi shi kadai dan haka sirrinsa ne. Jam'iyyun Adawa da kungiyoyin fafutuka da yawa sun nemi a bayyana wadannan bayanai inda suke cewa 'yan Najeriya na da damar sanin irin rayuwar da shugaban kasar yayi a baya.
Kalli Bidiyon: Sojoji da aka kama sun yi yunkurin yiwa shugaban kasar Nijar Juyin mulki

Kalli Bidiyon: Sojoji da aka kama sun yi yunkurin yiwa shugaban kasar Nijar Juyin mulki

Duk Labarai
An kama Sojoji da suka yi Yunkurin yiwa shugaba kasar Nijar Juyin mulki. Cikin sojojin da aka kama hadda mace. Rahotanni sun bayyana cewa, Daga cikin sojojin Gwamnati ne aka samu baraka suka bar wajan sa aka turasu aiki suka afkawa fadar shugaban kasar dan kwace iko da mulkin kasar. Sannan wasu daga cikinsu sun afkawa Filin sauka da tashi na jiragen saman kasar. Saidai An dakile wannan yunkurin inda Rahotanni suk ce lamura sun dawo daidai a Jamhuriyar Nijar din. https://twitter.com/KennedyWandera_/status/2093733601707737230