Monday, June 29
Shadow
Kalli Bidiyon: Ahmad XM ya bayyana wanda yayi nasarar samun kyautarsa ta Naira Miliyan 1

Kalli Bidiyon: Ahmad XM ya bayyana wanda yayi nasarar samun kyautarsa ta Naira Miliyan 1

Duk Labarai
Ahmad XM ya sanar da wanda ya lashe kyautar Miliyan 1da yace zai baiwa daya daga cikin mutanen dake comment dinsa. Wanda ya lashe wannan kudi shine Uzaifa Sabitu wanda ya bayyana cewa, ya dade yana son canja rayuwarsa inda yace idan ya samu kudin zai karfafa kasuwancinsa dasu. Ahmad XM yace masa ya tura masa da account dinsa kuma tuni ya saka masa kudin. https://twitter.com/i/status/2071194877916811543 Daga baya matashin ya bayyana a wani Bidiyo inda yakewa Ahmad XM Godiya. https://twitter.com/i/status/2071212241718755720
Kalli Bidiyon: Kikace kin tuba? Kwana biyu bayan da aka sakota daga ofishin HISBAH, Gorgeous ta saki sabon Bidiyo da ya jawo cece-kuce

Kalli Bidiyon: Kikace kin tuba? Kwana biyu bayan da aka sakota daga ofishin HISBAH, Gorgeous ta saki sabon Bidiyo da ya jawo cece-kuce

Duk Labarai
A kwana biyu da suka gabata ne dai muka ga Gorgeous a ofishin Hisbah inda ta bayyana nadamar abubuwan da ta yi a baya. Ta kuma roki masu tsaffin Bidiyon ta da su goge inda tace duk wanda bai goge ba, bata yafe masa ba. Saidai duk da haka sai gashi an ganta a wani Bidiyo tana rawa wadda wasu ke cewa bata dace ba. Wasu sun rika tambayarta a comment cewa, ba itace tace ta tubaba? https://www.tiktok.com/@gorgeous_ghurl/video/7656479168506481938?_r=1&_t=ZS-97bytxtaIo1
Wadanda suka je kallon wasannin kofin Duniya a kasar Amurka na kokawa da cewa Amurkawa sun cika roko

Wadanda suka je kallon wasannin kofin Duniya a kasar Amurka na kokawa da cewa Amurkawa sun cika roko

Duk Labarai
Wadanda suka je kallon wasannin kofin Duniya a kasar Amurka sun bayyana cewa, Amurkawa sun cika rokon kudi. Sun bayyana cewa ko ruwa mutum ya siyasa a shago sai kaji mutum yace wai a bashi kudi. A kasar Amurka, al'adar rokon Kwastoma kudi kyauta idan yayi siyayya ba sabuwar abu bace, da yawa zaka ga albashin da ake biyan ma'aikata babu yawa amma ta wajan kyautukan da ake basu anan suke samun kudade masu yawa da zasu iya rike kansu. Wasu sun yi bayanin cewa, su sunfi gane a gaya musu ainahin farashin kaya su saya maimakon a basu kaya da sauki amma kuma a rika rokonsu kudi.
Kalli Bidiyon: Bayan Na farko, Sabon Bidiyon Amal Umar Yafito inda aka ga Abokin yin fim dinta ya rungumeta

Kalli Bidiyon: Bayan Na farko, Sabon Bidiyon Amal Umar Yafito inda aka ga Abokin yin fim dinta ya rungumeta

Duk Labarai
A yayin kwanaki kadan da suka gabata, aka ga Tauraruwar fina-finan Hausa, Amal Umar a wani fim din kudancin Najeriya suka wasanni irin na ma'auarata suna kama hannu ita da Usman Uzee. A karo na biyu, Amal Umar ta sake yin wani abu da ya dauki hankula. An kuma sake ganinta inda Usman Uzee ya rungumeta. Lamarin ya jawo cece-kuce inda wasu ke cewa da suna mata kallon me hankali a cikin sabbin jaruman fina-finan Hausa. https://www.tiktok.com/@uzee_usman/video/7655611280719498518?_r=1&_t=ZS-97buEvKKoLs
Kalli Bidiyon: A karshe dai, Aminu Warkal ya bayyana laifin da matarsa ta mai ya saketa

Kalli Bidiyon: A karshe dai, Aminu Warkal ya bayyana laifin da matarsa ta mai ya saketa

Duk Labarai
Bayan da matarsa ta fito kafafen sada zumunta ta bayyana cewa ya saketa tsakar dare ya kuma ce ta fitar masa daga gida, Aminu Warkal ya bayyana dalilin da yasa ya mata hakan. A martaninsa, Aminu Warkal yace matarsa da suna zaune lafiya, kawai sai ta fito da wani sabon hali na rashin godiya kan dukkan abinda ya mata. Yace sannan babu wata magana me dadi dake shiga tsakaninsu. Yace hakanne da abu yayi kamari shine suka rabu. Yace babban abinda ya kawo rabuwar shine dabbobinsa da ta dauka ta sayar ba da izininsa ba, sannan ya kulle mata gida yace ta je ta dawo dasu amma taki. Saidai yace duk da wannan abu da ya faru tsakaninsu, har yanzu da zata kirashi tace yayi hakuri, da zai mayar da ita dakinta.
Bayan kama ‘yan kimmashin da suka dawo daga aikin Hajji a jihar Katsina, wanda kuma ake zargin gwamnatin jiharce ta dauki nauyin zuwansu Saudiyya, Gwamnatin Jihar Katsinar tace ba zata ce uffan ba kan lamarin

Bayan kama ‘yan kimmashin da suka dawo daga aikin Hajji a jihar Katsina, wanda kuma ake zargin gwamnatin jiharce ta dauki nauyin zuwansu Saudiyya, Gwamnatin Jihar Katsinar tace ba zata ce uffan ba kan lamarin

Duk Labarai
An kama shuwagabannin mutanen daji a filin jirgin sama na Umar Musa 'Yaradua dake jihar Katsina bayan sun dawo daga aikin hajjin bana Ministan harkokin cikin gida, Olubunmi Tunji-Ojo ya tabbatar da kamen inda yace an kamasu ne ranar 18 ga watan Yuni kuma tuni sun mikasu hannun jami'an DSS. Ministan yace sabuwar dokar katin dan kasa ta National Identity Management Commission (NIMC) ta taimaka sosai wajan kama mutanen. Saidai bai bayyana sunayen wadanda aka kama din ba. A hirarsa da BBCHausa, Kwamishinan harkokin cikin gida na jihar Katsina, Nasiru Mu’azu Danmusa ya tabbatar da kamen amma yace ba zasu ce komai akai ba saboda lamarine da ya shafi Gwamnatin tarayya Shi kuma Kwamishinan al'adu da yada labarai na jihar Katsina, Bala Salisu Zango ya bayyanawa Daily Trust cewa bai s...
”Yan Najeriya sune suka fi kowane mutane a Duniya kirki, da bayar da kyauta da sadaka ga mabukata>>Bincike

”Yan Najeriya sune suka fi kowane mutane a Duniya kirki, da bayar da kyauta da sadaka ga mabukata>>Bincike

Duk Labarai
Wani bincike da aka gudanar a kasashen Duniya guda 105 inda aka yi gwajin akan mutane 60,000 ya bayyana cewa, Najeriya ce kasa ta Daya a Duniya wadda mutanen ta suka fi kirki da taimakon mabukata da bayar da kyauta. Wata kungiyar bayar da Agaji ta Duniya, the Charities Aid Foundation (CAF) ce ta gudanar da wannan bincike. Binciken ya gano cewa a mafiya yawan kasashen da aka gidanar da binciken, an gano cewa, mutane suna bayar da kyauta ko sadakar kaso 1 cikin 100 na kudin da suke samu. Kasashen Africa ne kan gaba inda su kuma suke bayar da kaso 1.6 na kudin shigarsu sadaka, kyauta ko dan ci gaban addini. Kasashen turawa kuwa, suna bayar da kaso 0.6 cikin 100 ne na kudin shigarsu a matsayin sadaka ko kyauta. Saidai a gaba dayan kasashen duniyar, Najeriya ta zo ta daya inda mu...