Tuesday, August 4
Shadow
Anya Malam Pantami Baya shaye-shaye? Inji wannan Faston

Anya Malam Pantami Baya shaye-shaye? Inji wannan Faston

Duk Labarai
Malam ya je Bajoga yace musu Shekara 40 da ya wuce yakan tuko babanshi ya kawoshi Bajoga yayi hira da abokansa. Ya mayar dashi Gombe Shekarar shi nawane? 52 Idan ka cire shekaru 40 daga cikin shekarunsa saura shekaru 12. Yaran mu na da dan shekaru 12 zai iya tuka mota? Anya malam bai fara shaye-Shaye ba? Malam ya bata mu yi masa addu'a Allah ya dawo dashi hanya Inji Wannan Faston https://www.tiktok.com/@kibannachannels/video/7670256044773215506?_r=1&_t=ZS-98bw3lEGBVY
Kalli Bidiyon: Yanda Shugaban karamar hukumar Maigatari a jihar Jigawa ya kai ziyara wani shagon cacar kwallon kafa, Yace ba zai yadda ba sai an kulle shagon

Kalli Bidiyon: Yanda Shugaban karamar hukumar Maigatari a jihar Jigawa ya kai ziyara wani shagon cacar kwallon kafa, Yace ba zai yadda ba sai an kulle shagon

Duk Labarai
Shugaban karamar hukumar Maigatari a karamar hukumar Jigawa ya kai ziyara Shagon da akw buga Cacar kwallon kafa da aka bude. A wani Bidiyo da ya karade kafafen sada zumunta an ganshi yana fada yana tambayar cewa ina me shagon sannan ya tambayi sun yanki lasisi suka ce eh. Saidai yace ba zai yadda ba. https://twitter.com/i/status/2084565176188105108
Wasu kungiyoyi masu saka ido a harkokin siyasa daga jihar Gombe sun yi Allah wadai da kalaman Dan takarar Gwamna na jam’iyyar PDP, Farfesa Isa Ali Pantami inda sukace ya daina kalaman da zasu iya kawo rudani

Wasu kungiyoyi masu saka ido a harkokin siyasa daga jihar Gombe sun yi Allah wadai da kalaman Dan takarar Gwamna na jam’iyyar PDP, Farfesa Isa Ali Pantami inda sukace ya daina kalaman da zasu iya kawo rudani

Duk Labarai
Gamayyar Kungiyoyin dake saka ido akan harkokin siyasa a jihar Gombe me suna The Gombe State Coalition of Political Civil Societies and Association ta yi Allah wadai da kalaman dan takarar gwamnan jihar a karkashin jam'iyyar PDP, Farfesa Isa Ali Pantami. Kungiyar tace kalaman da Dan takarar yayi a ziyarar da ya kai karamar hukumar Dukku abin damuwa ne kuma ya kamata ya kiyaye. Kungiyar tace dukka 'yan takarar ya kamata su kiyaye kalamansu da yanayin ma'amalarsu dan a samu siyasa me tsafta. Kungiyar tace Jihar Gombe an santa da zaman lafiya da fahimtar juna suna kira ga 'yan siyasar kada su kawo rudanin da zai canja hakan.
Kalli Bidiyon: Budurwar Dan wasan Faransa Micheal Olise, Fatima tace ya barta da Hidimtawa dan gaba da fatiha da suka haifa ita kadai baya aika mata da tallafin komai

Kalli Bidiyon: Budurwar Dan wasan Faransa Micheal Olise, Fatima tace ya barta da Hidimtawa dan gaba da fatiha da suka haifa ita kadai baya aika mata da tallafin komai

Duk Labarai
Tsohuwar budurwar dan kwallon kasar Faransa, Michael Olise me suna Fatima tace dan da suka haifa tare ita kadai ke kula dashi. Tace Olise duk da yayi alkawari amma baya tura mata tallafin Euro 2000 da ya mata Alkawari. Tace ya amince da cewa dansa ne kuma lauyoyinsa sun san da maganar amma yaki amincewa da bayar da kudin kula da dan. https://twitter.com/i/status/2084566424337432924
Kalli Bidiyon: Yanda Shaikh Alkali Zaria yana tsaka da wa’azi a Kano aka dauke wuta, yace ku haska Kano ne Kano ne, sannan ya saka wayarsa a Aljihu

Kalli Bidiyon: Yanda Shaikh Alkali Zaria yana tsaka da wa’azi a Kano aka dauke wuta, yace ku haska Kano ne Kano ne, sannan ya saka wayarsa a Aljihu

Duk Labarai
Babban Malamin Addinin Islama, Sheikh Alkali Zaria ya bayyana a wani Bidiyo yana wa'azi a Kano. Saidai an dauke wuta, inda aka ji shi yana cewa, ku haska, Kano ne Kano ne, Sannan an ganshi yana saka wayarsa a aljihu. https://www.tiktok.com/@akafawee/video/7669727894654012690?_r=1&_t=ZS-98bQti2kIK4
Shi Shugaba Tinubu Babban Mutum ne kuma dan baiwa, irin su basa bukatar su je aji kamin su samu takardar kammala Firamare ko Sakandare>>Inji Ministan sufuri jiragen sama, Festus Keyamo

Shi Shugaba Tinubu Babban Mutum ne kuma dan baiwa, irin su basa bukatar su je aji kamin su samu takardar kammala Firamare ko Sakandare>>Inji Ministan sufuri jiragen sama, Festus Keyamo

Duk Labarai
Ministan Sufurin Jiragen sama, Festus Keyamo ya bayyana cewa, bayyana cewa, irin su shugaban kasa, Bola Ahmad Tinubu mutane ne na musamman 'yan Baiwa. Wanda yace a zamanin da irin su basa bukatar sai sun je aji kamin su samu takardar kammala Firamare ko sakandare ta GCE. Yace daga gida suke rubuta jarabawa sai a basu takardar kammala makarantun. Ya bayyana hakane a gidan Talabijin na Arise TV yayin da ake ganawa dashi game da maganar cece-kuce da akw na cewa shugaban kasa, Bola Ahmad Tinubu bai baiwa INEC takardun kammala Firamare da sakandare ba.