Thursday, April 2
Shadow
Nine Halastaccen Shugaban Jam’iyyar ADC, kuma rade-radin da ake cewa wai na ajiye mukami na karyane, sai naga bayansu>>Inji Nafiu Bala da ya kai su Atiku, Kwankwaso, El-Rufai da Malami kotu yace shine shugaban ADC kwace suka masa

Nine Halastaccen Shugaban Jam’iyyar ADC, kuma rade-radin da ake cewa wai na ajiye mukami na karyane, sai naga bayansu>>Inji Nafiu Bala da ya kai su Atiku, Kwankwaso, El-Rufai da Malami kotu yace shine shugaban ADC kwace suka masa

Duk Labarai
Nafiu Bala wanda yake ikirarin shine halastaccen shugaban rikon gwarya na jam'iyyar ADC ya bayyana cewa, rade-radin da ake yi cewa ya dauka daga mukaminsa ba gaskiya bane. Nafiu Bala dai shine ya kawo rikici a jam'iyyar ADC inda ya kai jiga-jigan Adawa kotu. Yace da tsohon shugaban jam'iyyar zai sauka, shi ya barwa rikon kwarya. https://twitter.com/i/status/2039666201173934172
Ku dawo jam’iyyar PRP tunda ADC ta rikice>>Inji Shugaban jam’iyyar PRP

Ku dawo jam’iyyar PRP tunda ADC ta rikice>>Inji Shugaban jam’iyyar PRP

Duk Labarai
Shugaban jam'iyyar PRP James Adeshina ya yi kira ga su Atiki Abubakar, da Malam Nasiru Ahmad El-Rufai, da Dr. Rabiu Musa Kwankwaso, Abubakar Malami da sauransu cewa, su bar jam'iyyar ADC su dawo PRP tunda jam'iyyar ta ADC ta rikice. Ya bayyana hakane ga manema labarai inda yace abin takaici ne ganin yanda babbar jam'iyyar adawa a Najeriya ADC ta shiga rikici. Wani me suna Nafiu Bala da ya kai su Atikun kotu ya bayyana cewa, shine shugaban jam'iyyar ta ADC ba David Mark ba inda hakan yasa INEC ta cire sunan David Mark daga kundin tattara bayananta har sai an kammala shari'ar a kotu.
Da Duminsa: An jibge Jami’an tsaro a ofishin INEC dan hana Jam’iyyar ADC Zàngà-zàngà

Da Duminsa: An jibge Jami’an tsaro a ofishin INEC dan hana Jam’iyyar ADC Zàngà-zàngà

Duk Labarai
Rahotanni sun bayyana cewa, an jibge jami'an tsaro a ofishin INEC dake Abuja dan hana jam'iyyar ADC zanga-zanga. Jam'iyyar ADC ta yi barazanar yin zanga-zanga kan cire sunayen shuwagabannin ta daga shafin INEC. Dan hakane aka jibge jami'an tsaron. An ga hotunan jami'an tsaro dauke da muggan makamai da tankokin ruwan zafi zagaye da ofishin INEC.
Ban taba ganin Azzalumai irin su Atiku da Kwankwaso, da El-Rufai ba, Ta yaya zasu zo su iskeni a gidana suce zasu yi fada dani kuma su yi nasara>>Inji Wanda yace shine shugaban ADC ba David Mark ba watau Nafiu Bala

Ban taba ganin Azzalumai irin su Atiku da Kwankwaso, da El-Rufai ba, Ta yaya zasu zo su iskeni a gidana suce zasu yi fada dani kuma su yi nasara>>Inji Wanda yace shine shugaban ADC ba David Mark ba watau Nafiu Bala

Duk Labarai
Wanda ke ikirarin cewa shine shugaban jam'iyyar ADC, Nafiu Bala wanda kuma ya kai su Atiku, Kwankwaso, Peter Obi, da David Mark, da Rauf Aregbesola da sauransu kotu yana neman a kwace shugabancin jam'iyyar a bashi watau Nafiu Bala yace bai taba ganin zalunci irin na su Atikun ba. Ya bayyana hakane a wata hira da aka yi dashi wadda ta watsu a kafafen sada zumunta. Yace ta yaya mutane zasu zo har gidansa su sameshi suce zasu yi fada dashi kuma su yi nasara?
Yanda jigon jam’iyyar APC daga jihar Kano ya rasu a Otal din Abuja

Yanda jigon jam’iyyar APC daga jihar Kano ya rasu a Otal din Abuja

Duk Labarai
Rahotanni sun bayyana cewa, mataimakin sakataren jam'iyyar APC ta jihar Kano, Abdulsalami Ginsau ya rigamu gidan gaskiya a otal din Chida dake Utako, Abuja. Rahoton yace Abdulsalami shine ke kula da masaukin baki na wakilan jam'iyyar APC daga jihar Kano a babban taron jam'iyyar da aka yi a Abuja. Kuma ya je otal din inda kama duka dakunan otal din guda 150. Saidai bayan da gari ya waye aka tafi wajan taron jam'iyyar APC din sai ba'a ganshi ba, anan aka fara bincike. Shugaban jam'iyyar APC a jihar Kano, Umar Haruna Doguwa ya bayyana cewa, sun kai korafi ofishin 'yansanda dake Utako, yace sai 'yansandan suka ce an kawo musu rahoto daga Otal Chida, ko da suka je sai suka ga Abdulsalami ne. 'yansanda sun ce sun fara bincike kan lamarin. Itama wata majiya daga otal din ta tabb...
Kalli Bidiyon: Matasa Musulmai na Jis na shan yabo saboda yanda suka rika boye Kiristoci yayin da Rikici ya barke, daga baya suka rika mikasu hannun jami’an tsaro

Kalli Bidiyon: Matasa Musulmai na Jis na shan yabo saboda yanda suka rika boye Kiristoci yayin da Rikici ya barke, daga baya suka rika mikasu hannun jami’an tsaro

Duk Labarai
Bidiyo kala-kala na ta yawo a kafafen sada zumunta inda aka ga Musulmai a Jos na boye Kiristoci a yayin da rikici ya barke. An ga yanda daga baya suke mika Kiristocin a hannun jami'an tsaro. https://twitter.com/i/status/2039355260716589252 Lamarin ya jawo musu yabo da kuma Addu'ar Allah ya kawo mana zaman Lafiya. https://twitter.com/i/status/2039395012455084293
Babban yaron tsohon Ministan tsaro, Abubakar Badaru ya fice daga jam’iyyar APC

Babban yaron tsohon Ministan tsaro, Abubakar Badaru ya fice daga jam’iyyar APC

Duk Labarai
Daya daga cikin manyan yaran tsohon Ministan tsaro, Abubakar Badaru me suna Hon. Zakari Kafin Hausa ya fice daga jam'iyyar APC. A sakon da ya fitar dake ta yawo a kafafen sada zumunta yace ya fice daga jam'iyyar APC saboda tana saka mutane cikin damuwa. Sannan yayi kira ga duka mabiyansa suma su fice daga jam'iyyar. https://twitter.com/i/status/2039457227031900603