Friday, July 10
Shadow
Wata Sabuwa Kalli Bidiyon: Mata 4 sun fitar da update din malamin jami’ar da akawa na jaki saboda neman matar aure

Wata Sabuwa Kalli Bidiyon: Mata 4 sun fitar da update din malamin jami’ar da akawa na jaki saboda neman matar aure

Duk Labarai
Rahotanni sun bayyana cewa, wasu mata 4 sun fito suma sun bayyana cewa malamin jami'ar MAUN dake Kano da aka lakadawa na jaki saboda zargin neman matar aure suna ya nemesu. Matan sun bayyana hakane ga shahararren mawallafin labarai na kafafen sada zumunta, watau, Abis Fulani. Saidai Abis Fulani yace ba zai wallafa zargin da wadannan matan suka kai masa ba inda yace baya son shafinsa ya zama wajan tone-tonen Asirin mutane. Yace matan su kaiwa hukumar makarantarsu korafi. Sannan ya bayyana cewa jami'ar MAUN dake Kano ta fitar da bayanai cewa malamin da aka lakadawa dukan ya daina mata aiki dama aikin wucin gadi ne ya mata. https://www.tiktok.com/@abis_fulani/video/7660643441885416736?_r=1&_t=ZS-97uiA4u0IHl
Kalli Bidiyon: Sumbatar juna da Gfresh Al-amin da matarsa Sadiya Haruna suka yi a bainar jama’a ya jawo cece-kuce

Kalli Bidiyon: Sumbatar juna da Gfresh Al-amin da matarsa Sadiya Haruna suka yi a bainar jama’a ya jawo cece-kuce

Duk Labarai
An ga Taurarun Tiktok, Sadiya Haruna da Gfresh Al-amin suna Bidiyo a tsakaninsu bayan da yace ya mayar da ita. A baya dai an ga yanda Gresh ya taro matar tasa a Filin jirgi bayan ta dawo daga Umara. A wannan sabon Bidiyon an gansu ne suna cin abinci a wani gidan sayar da abinci wanda Gfresh yace kyauta aka basu. Sannan kuma an ga suna sumbatar juna a bainar jama'a wanda hakan ya jawo cece-kuce https://www.tiktok.com/@gfreshfanpage/video/7660647942029757703?_r=1&_t=ZS-97ugOjQDavV
Kalli Bidiyon: Ina neman mijin aure, kuma zan bashi jari da Sadaki, idan ka matsa sai ka biya sadaki, Salati kawai nake son kawa Annabi(Sallallahu Alaihi Wasallam) inji Wanan matar

Kalli Bidiyon: Ina neman mijin aure, kuma zan bashi jari da Sadaki, idan ka matsa sai ka biya sadaki, Salati kawai nake son kawa Annabi(Sallallahu Alaihi Wasallam) inji Wanan matar

Duk Labarai
Wannan wata matace data dauki hankula bayan data fito ta bayyana cewa, tana neman mijin aure. Matar tace duk me sonta idan bashi da sana'a zata bashi jari. Sannan zata bashi sadaki inda tace amma idan ya dage sai ya biya sadaki, abinda kawai take son ya biya shine ya wa Annabi(Sallallahu Alaihi Wasallam) Salati. Ta bayyana hakane a shafinta na Tiktok inda tace duk wanda ke sonta ya ajiye mata lambar wayarsa a comment. https://www.tiktok.com/@mominjss/video/7660525260772691207?_r=1&_t=ZS-97ueHJXhJ4v
Ta kusa da Atiku, Dr. Aslam Aliyu data ce ta koma APC tace a daina damunta idan ba haka ba zatawa Atiku tonon silili

Ta kusa da Atiku, Dr. Aslam Aliyu data ce ta koma APC tace a daina damunta idan ba haka ba zatawa Atiku tonon silili

Duk Labarai
Dr. Aslam Aliyu wadda ta kusa da Atiku Abubakar amma yanzu ta fice daga jam'iyyar ADC ta koma jam'iyyar APC tace yaransa su daina damunta. Tace Atiku Abubakar yaci amanarta ne shiyasa ta barshi. Tace kuma da ake zaginta dan ta bar jam'iyyar ADC, bata zagi Atiku ba, dan Atiku daya koma APC me yasa shi ba'a zaginsa? Tace kuma na kusa da Atiku basu kaunarsa. https://www.tiktok.com/@expressmediahausa/video/7660623483247856914?_r=1&_t=ZS-97uVdjS2MUf
Kalli Bidiyon: Malamai da yawa a Arewa addinin karya suke koyawa, ba haka ake Musulunci a sauran kasashen Duniya ba>>Inji Soja Boy

Kalli Bidiyon: Malamai da yawa a Arewa addinin karya suke koyawa, ba haka ake Musulunci a sauran kasashen Duniya ba>>Inji Soja Boy

Duk Labarai
Tauraron mawakin Hausa, Soja Boya ya caccaki malaman addinin Addinin Musulunci inda yace addinin Karya suke koyarwa mutanen Arewa. Yace irin yadda Malamai ke koyar da Musulunci a Najeriya babu inda ake koyar da Musulunci haka a kasashen Duniya hatta kasashen Larabawa. Yace to shin Shi bahaushe yana tunanin shi kadaine zai shiga Aljanna kenan. Soya boy yace duk malamin da ya kara ce masa ba'a zo zama Duniya ba to uwarsa suka zo yi Duniya? Sannan yace kwanannan zasu fara cin uwar malamai. https://www.tiktok.com/@officialsojaboyy/video/7660652503427501332?_r=1&_t=ZS-97uQR1RDrYS
Kalli Bidiyon: Yanda ‘yan majalisa suka ki amincewa da Yusuf Gadgi bayan da yace ya kamata su gayyaci shugaba Tinubu ya musu bayani kan matsalar tsaro

Kalli Bidiyon: Yanda ‘yan majalisa suka ki amincewa da Yusuf Gadgi bayan da yace ya kamata su gayyaci shugaba Tinubu ya musu bayani kan matsalar tsaro

Duk Labarai
'Yan majalisa da yawa ne suka ki amincewa da bukatar abokin aikinsu Yusuf Gadgi bayan da yayi kiran cewa ya kamata su gayyaci shugaban kasa, Bola Ahmad Tinubu ya musu bayani kan matsalar tsaro. A Bidiyon da yake ta yawo a kafafen sada zumunta, An ga Yusuf Gadgi a mike yana jawabin cewa a gayyaci shugaba Tinubu. Saidai an ji da yawa 'yan majalisar na masa ihun cewa basu amince ba ya zauna. https://twitter.com/i/status/2075236629850071133 Hakan ya baiwa 'yan Najeriya da yawa mamaki inda wasu ke tambayar shin 'yan majalisar wa suke wakilta kuma zaman me suke a majalisar?
Kalli Bidiyon Yanda Kyawun dan Kwallon Najeriya, Maduka Okeke ya rikita matan turawa sai rububi suke akansa

Kalli Bidiyon Yanda Kyawun dan Kwallon Najeriya, Maduka Okeke ya rikita matan turawa sai rububi suke akansa

Duk Labarai
Dan kwallon Najeriya, Maduka Okeke ya dauki hankulan matan turawa inda suke ta yabawa da kyawunsa. Ya halarci wajan taron nuna kayan sawa na kawa a kasar Faransa inda acanne suka hadu da mawakiyar Amurka, Cardi B inda itama ta yaba da kyawunsa. https://twitter.com/i/status/2075297848715878545 Daga nan ne fa hankalin matan Amurkawa ya karkata zuwa garesu suke ta yabawa da kyawunsa. https://twitter.com/i/status/2075191445170880824 https://twitter.com/i/status/2075283955910115703 https://twitter.com/i/status/2075132309012103576 https://twitter.com/i/status/2075129474858074240