Farashin dala a kasuwar Chanji ta Gwamnati a yau, Laraba, 22 ga watan Afrilu ya kai Naira 1,348.77 NGN akan kowace dala.
Farashin ya dan sauka zuwa Naira 1,346.30 NGN kamin daga baya ya sakw hawa.
A kasuwar bayan fage kuwa ta garuruwan Abuja, Legas da Kano, Farashin dalar ya kai Naira 1,450 NGN zuwa naira 1,470 NGN akan kowace dala.
Tauraron Tiktok, Gfresh Al-amin yace Hudubar Adam A. Zango ta yi aiki akansa inda yace shima daga yau ya daina tallar matarsa a kafafen sada zumunta.
Yace duka abokansa na da mata amma babu wanda yake ganin matansa sai shi sakarai ake ganin matarsa.
Yace ya hau shafinta na Tiktok ya goge Bidiyon data dora sannan wanda take friends dasu ma ya gogesu.
https://www.tiktok.com/@gfreshfanpage/video/7631339680214076680?_r=1&_t=ZS-95kERbNKtg9
A yayin da matsalar rashin wutar Lantarki ta damu Al'ummar Najeriya, suka koma amfani da Solar.
Wani sabon salo shine da aka ga jami'an gwamnati sun fara bi gidaje dake amfani da Solar suna cewa, a basu harajin Amfani da Solar.
Lamarin ya fara a Legas ne inda wani Magidanci yace ba zai biya ba bayan da aka rutsashi aka ce wai sai ya biya Harajin saka Solar.
Bidiyon faruwar lamarin ya karade kafafen sadarwa inda ake ta cece-kuce akai.
https://twitter.com/i/status/2046706370271981996
Shahararren ma'aikacin gidan rediyo daga kudancin Najeriya,Roby Ekpo ya bayyana cewa dalilin da yasa suka rabu da matarsa shine baya iya biya mata bukatar aure.
Yace shi ba yaro bane, yayi aure yana da shekaru 37.
Yace matarsa amma kullun take son su rika kwanciyar aure.
Yace amma shi ba zai iya ba inda yace saidai sau biyu a sati amma taki amincewa da hakan.
Yace dole saidai rabuwa suka yi
Wannan wani dan siyasa ne a jihar Kwara da ya so fitowa takarar dan majalisa jiha amma aka cire sunansa daga cikin jerin 'yan takarar.
Hakan yasa ya fashe da kuka yana korafi.
Rahotanni sun ce a baya mawaki ne dake yiwa 'yan siyasa waka.
https://twitter.com/i/status/2046606887458599014
A dazune dai hutudole ya kawo muku rahoton cewa, Shugaban kasa, Bola Ahmad Tinubu ya sauke ministan kudi, Wale Edun daga mukaminsa.
Gwamnati dai bata bayyana dalilin sauke shi daga mukamin nasa ba a hukumance.
Lamarin ya zowa mutane da mamaki duk da yake cewa a kwanakin baya an yi ta rade-radin cewa, Ministan yayi fama da rashin lafiya.
Saidai a yanzu a kafafen sada zumunta, ana ta yada wani Bidiyo daya nuna shugaban kasa, Bola Ahmad Tinubu yana cewa sun cimma yawan kudin shiga da suke nema a shekarar 2025.
Saidai a wani Bidiyo daban kuma, an ga Ministan kudin, Wale Edun na cewa Tiriliyan 40 suke nema a shekarar 2025 amma kudin shiga Tiriliyan 10 kacal suke tsammani.
Wannan magana ta ci karo data shugaban kasa, wadda wannan yasa wasu ke ta hasashen cewa, dalili kenan da yasa...
Rahotanni sun bayyana cewa, matatar man fetur ta Dangote zata fara hako danyen man fetur.
Mataimakin Dangote, Devakumar Edwin ne ya bayyana hakan a wata ganawa da aka yi dashi inda yace har sun fara gwajin hako man fetur din.
Yace Hakowar ta Gwaji zata dauki akalla zuwa Sati 3 ko 4.
Yace daga nan kuma zasu fara hako man sosai ta yanda zasu rika sayar dashi ko amfani.
Shugaban kasa, Bola Ahmad Tinubu ya sauke Ministan Kudi, Wale Edun da Ministan Gidaje Da ci gaban birane Umar Dangiwa.
Sakataren Gwamnati, Sanata George Akume ne ya bayyana hakan a wata sanarwa da ya fitar.
An baiwa Wale Edun umarnin ya mikawa karamin Ministan kudi, Mr. Taiwo Oyedele ragamar ma'aikatar.
Hakanan shugaba Tinubu ya nada Mr. Muttaqha Rabe Darma (PhD) a matsayin Ministan Gidaje da ci gaban birane.
Rahotanni sun ce a yaune Nafiu Bala Gombe yake gudanar da babban taron jam'iyyar ADC tsaginsa inda zasu zabi shuwagabannin jam'iyyar.
Saidai Bidiyon dake ta yawo a kafafen sada zumunta aun nuna cewa babu kowa a wajan taron
Wasu rahotanni sun ce har Naira Dubu hamsin ake baiwa duk wanda ya yadda zai je wajan taron amma duk da haka babkowa.
https://twitter.com/i/status/2046526118052651202
Da alama dai Tsohon Gwamnan jihar Kaduna, Malam Nasiru Ahmad El-Rufai ba zai samu damar halartar zaben fidda gwani na jam'iyyar ADC ba.
Saboda Mai shari'a Darius Khobo na babbar kotun jihar Kaduna ya sake daga sauraron belinsa sai satin farko na wajan Yuni.
ICPC na ci gaba da tsare malam Nasiru Ahmad El-Rufai inda ake zarginsa da almundahanar kudade da aikata ba daidai ba da mukamin da ya samu na Gwamna da sauransu.
Jam'iyyar ADC dai ta tsayar da karshen watan Afrilu zuwa Mayu dan gudanar da zaben fidda gwani.