Tuesday, May 19
Shadow
Kalli Bidiyon: A karin farko, An samu mawakiya Bahaushiya ta yi waka me salo irin na turawa, inda aka ganta tana wakar a bandaki yayin da take wanka babu komai a jikinta

Kalli Bidiyon: A karin farko, An samu mawakiya Bahaushiya ta yi waka me salo irin na turawa, inda aka ganta tana wakar a bandaki yayin da take wanka babu komai a jikinta

Duk Labarai
Wata mawakiya Bahaushiya Ta bayyana inda ta dakko salon waka irin na turawa. An ganta tana waka a bandaki yayin da take wanka babu kaya a jikinta. Lamarin ya dauki hankula sosai. Da yawa dai sun ce hakan bai dace ba. https://www.tiktok.com/@batulayaramanacemana/video/7641094105384226069?_r=1&u_code=ejaikd8elj8058&preview_pb=0&sharer_language=en&_d=ejaij098emc1h5&share_item_id=7641094105384226069&source=h5_m&timestamp=1779229726&user_id=7483197776647635989&sec_user_id=MS4wLjABAAAAN7fVbcc0mzRzgIxdVwTekj-Bzgfq381B8aILPWs15fqP6aFNZ5GwIpbLEwMTYvVW&item_author_type=2&social_share_type=0&utm_source=copy&utm_campaign=client_share&utm_medium=android&share_iid=7625183675001341712&share_link_id=db037f47-b1a0-4ee9-98c8-83bf8...
Bayani Dalla-dalla: Ji yanda aka kama wani Kwarto a cikin jakar Ghana Must Go a dakin matar aure kamar yanda HISBAH suka sanar

Bayani Dalla-dalla: Ji yanda aka kama wani Kwarto a cikin jakar Ghana Must Go a dakin matar aure kamar yanda HISBAH suka sanar

Duk Labarai
Hukumar HISBAH ta jihar Kebbi ta sanar da kama wani Kwarto a cikin dakin matar aure a boye a cikin jakar Ghana Must Go. Lamarin ya farune ranar Litinin, 18 ga watan Mayu a unguwar Badariyya dake Birnin Kebbi. Jama'ar Unguwane suka lura da mutumin ya shiga gidan matar auren inda suka gaggauta sanar da hukuma. Daraktan HISBAH na jihar, Sirajo Kamba ya tabbatar da faruwar lamarin, kamar yanda daily Trust ta ruwaito. Yace da jami'an sa suka je gidan suka nemi izinin shiga, matar taki amincewa amma da aka dade ana turjiya sai ta amince. Aikuwa da bincike yayi tsanani sai ga Kwarto a cikin jakar Ghana Must Go. An kamasu duka aka tafi aka fara bincike inda duka suka amsa laifin da ake zarginsu da aikatawa na soyayya. Kamba yace za'a gurfanar dasu gaban kotu domin yanke musu...
Kalli Bidiyon rawar rashin Kunya da wasu ‘yan Matan Arewa suka yi da ta jawo cece-kuce

Kalli Bidiyon rawar rashin Kunya da wasu ‘yan Matan Arewa suka yi da ta jawo cece-kuce

Duk Labarai
Wasu 'yan mata da aka rika bayyana cewa daga Arewa suka fito sun dauki hankula bayan wata rawa da suka yi data jawo cece-kuce a kafafen sada zumunta. Da yawa dai sun ce rawar da suka yi bata kamata ba musamman ganin cewa sun saka kayan dake nuna kamala. https://twitter.com/i/status/2056010567135981797 Wasu kuma sun rika bayyana cewa, Shiga me kamala ba ita ke nuna mutum na da tarbiyya ba.
Kalli Bidiyon: Kalaman da Gwamnan Kano, Abba Kabir Yusuf ya yi akan Kwankwaso da wasu ke cewa basu dace ba

Kalli Bidiyon: Kalaman da Gwamnan Kano, Abba Kabir Yusuf ya yi akan Kwankwaso da wasu ke cewa basu dace ba

Duk Labarai
Gwamnan Kano, Abba Kabir Yusuf ya bayyana cewa idan babba bai kama girmansa ba, Karami ba zai ji kunyar shi ba. Gwamnan ya bayyana hakane akan takaddamar dake tsakaninsa da Tsohon Maigidansa, Kwankwaso wanda tun bayan da ya bar Jam'iyyar NNPP zuwa APC dangantaka ta yi tsami tsakaninsu. Abba ya bayyana mamakin yanda Kwankwaso dake da shekaru 69 yake ce masa yaro saboda yana da shekaru 63. https://twitter.com/i/status/2056469075836989481
Kalli Bidiyon: Yanda Tsohon Gwamnan Kaduna, Malam Nasiru Ahmad El-Rufai yaki sauka daga motar DSS yace saidai su fitar dashi da Qarfi

Kalli Bidiyon: Yanda Tsohon Gwamnan Kaduna, Malam Nasiru Ahmad El-Rufai yaki sauka daga motar DSS yace saidai su fitar dashi da Qarfi

Duk Labarai
Malam Nasiru Ahmad El-Rufai ya ki sauka daga motar DSS ya ce saidai a fitar dashi da Karfi. Lamarin ya farune bayan da kotu ta bayar da belinsa, amma maimakon ICPC su tafi dashi, Sai DSS suka tafi dashi. Dan hakane malam yace ai ba haka doka tace ba, ko da aka je ofishin DSS sai yaki fita daga motar yace saidai idan da karfin tuwo za'a fitar dashi. Matarsa ce ta bayar da wannan labari a wata hira da manema labarai suka yi da ita. Kalli Bidiyon a kasa: https://twitter.com/i/status/2056462808078840060
Mahaifina wan Farfesa Isa Ali Pantami ne uwa daya uba daya amma bai taba amfanar dani da komai ba>>Inji Wannan bawan Allahn

Mahaifina wan Farfesa Isa Ali Pantami ne uwa daya uba daya amma bai taba amfanar dani da komai ba>>Inji Wannan bawan Allahn

Duk Labarai
Wani mutum ya bayyana inda yake ikirarin cewa, Mahaifinsa da mahaifin Farfesa Sheikh Hon. Isa Ali Pantami 'yan uwan junane. Yace amma Pantami bai taba amfanar dashi da komai ba. Ya bayyana hakane a wata hira da aka yi dashi wadda ke ta yawo a kafafen sadarwa. https://www.tiktok.com/@sheikh_hafram_khaleel_/video/7640815983120141586?_r=1&_t=ZS-96StuefuyaP
Kalli Bidiyon: Yanda nake son Zarmalulu haka nake son aikina>>Inji Shahararriyar me wanke gidaje, Maryam

Kalli Bidiyon: Yanda nake son Zarmalulu haka nake son aikina>>Inji Shahararriyar me wanke gidaje, Maryam

Duk Labarai
Tauraruwar me wanke gidaje ta Abuja me suna Maryam ta bayyana cewa, Yanda take son Zarmalulu haka take son aikinta. Ta bayyana hakane a shafinta na sada zumunta wanda hakan ya jawo cece-kuce inda wasu ke cewa bai kamata ta yi maganar ba. https://www.tiktok.com/@mbacleaningandlaundry/video/7640915989831388423?_r=1&_t=ZS-96Ssgvv4w5Z
Da Duminsa: Na samu bayanai masu inganci cewa Gwamnati na shirin shyèkyè Malam Nasiru Ahmad El-Rufai>>Inji Timi Frank

Da Duminsa: Na samu bayanai masu inganci cewa Gwamnati na shirin shyèkyè Malam Nasiru Ahmad El-Rufai>>Inji Timi Frank

Duk Labarai
Tsohon sakataren yada labarai na jam'iyyar APC, Timi Frank ya bayyana cewa, ya samu bayanai masu inganci dake tabbatar da cewa, Gwamnatin tarayya na shirin Shyèkyè malam Malam Nasiru Ahmad El-Rufai. Ya bayyana cewa ya samu bayanan ne daga wata majiya ta tsaro. Inda yayi zargin cewa, za'a sako Malam Nasiru Ahmad El-Rufai amma za'a bashi wani abu wanda bayan an sakeshi ba zai dade ba zai koma ga Allah. Yace a tabbatar da lafiyar malam Nasiru Ahmad El-Rufai kuma duk abinda ya sameshi alhaki akan Gwamnati ne.
Kalli Bidiyon Da Duminsa: Wani ya tsere da kayan zabe a mazabar Farfesa Isa Ali Pantami, ba’a yi zaben fidda Gwani ba

Kalli Bidiyon Da Duminsa: Wani ya tsere da kayan zabe a mazabar Farfesa Isa Ali Pantami, ba’a yi zaben fidda Gwani ba

Duk Labarai
Rahotanni daga Pantami Jihar Gombe na cewa, sakataren jam'iyyar na yankin ne ya tsere da kayan zaben ba'a samu an gudanar da zaben fidda gwani ba a mazabar. Daya daga cikin yaran Farfesa Pantamin ne ya fito kafafen sada zumunta yana bayyana hakan. An ga Bidiyon sa yana cewa basu yi zaben fidda gwani nba, sakataren ne ya tsere da kayan zaben a kan mashin da wani. https://twitter.com/i/status/2055649488316854439