Monday, February 16
Shadow
Kalli Bidiyon yanda shugaban jam’iyyar APC a jihar Kano, Abbas ke korafin cewa babu mutane da yawa a wajan taron karbar Gwamna Abba Kabir Yusuf zuwa APC

Kalli Bidiyon yanda shugaban jam’iyyar APC a jihar Kano, Abbas ke korafin cewa babu mutane da yawa a wajan taron karbar Gwamna Abba Kabir Yusuf zuwa APC

Duk Labarai
An ga Shugaban jam'iyyar APC na jihar Kano, Abdullahi Abbas na bayyana rashin jin dadinsa kan yanda ba'a tara mutane da yawa ba a wajan karbar Gwamna Abba Kabir Yusuf zuwa jam'iyyar APC. Mataimakin shugaban kasa, Kashim Shettima ne ya je wajan Taron a Kano. https://twitter.com/i/status/2023410837831221607
Kalli Bidiyon: An bamu kudi mu yi zàngà-zàngà neman a hukunta malam Nasiru Ahmad El-Rufai amma da na gano akanshine zamu yi nace ba zan yi ba saboda inasonshi>>Inji Daya daga cikin masu Zàngà-zàngàr neman a Hukunta El-Rufai

Kalli Bidiyon: An bamu kudi mu yi zàngà-zàngà neman a hukunta malam Nasiru Ahmad El-Rufai amma da na gano akanshine zamu yi nace ba zan yi ba saboda inasonshi>>Inji Daya daga cikin masu Zàngà-zàngàr neman a Hukunta El-Rufai

Duk Labarai
Daya daga cikin wadanda suka fito yin zanga-zangar neman a hukunta malam Nasiru Ahmad El-Rufai ya bayyana cewa kudi aka basu. Yace amma da ya fito yana akan Malam Nasiru ne zasu yi zanga-zangar sai ya ce ba zai yi ba saboda yana son malam. https://twitter.com/i/status/2023341053533729017
Kalli Bidiyon da Duminsa:Yanda rikici ya barke a majalisar Dattijai hadda kai Nàushy yayin da Sanata Natasha Akpoti ta ke fada da wani sanata

Kalli Bidiyon da Duminsa:Yanda rikici ya barke a majalisar Dattijai hadda kai Nàushy yayin da Sanata Natasha Akpoti ta ke fada da wani sanata

Duk Labarai
Rahotanni daga majalisar Dattijai sun bayyana cewa, sanata Natasha Akpoti daga jihar Kogi ta shiga ofishin sanata Titus Zam inda take ta babatu akan cewa an cire sunanta daga kwamitin da zasu kula da kasafin kudin hukumar ci gaban Arewa ta tsakiya. Sanata Natasha Akpoti ta rika fadin cewa, ba zata amince da wannan abu ba inda aka ana rike wani dake kokarin kai Naushi. Sanata Natasha Akpoti dai tace wannan daya ne daga cikin kokarin da ake na tauyewa mutanen mazabarta hakkinsu, tace babu wani sanatan da yafi wani, duk daya suke. https://twitter.com/i/status/2023404817264320577 https://twitter.com/i/status/2023416181357695318
Kalli Bidiyon: Idan kana Azumi sai ka yi niyyar tarawa da iyalinka, ko da baka aikata ba, Azuminka ya karye>>Inji Wannan malamin

Kalli Bidiyon: Idan kana Azumi sai ka yi niyyar tarawa da iyalinka, ko da baka aikata ba, Azuminka ya karye>>Inji Wannan malamin

Duk Labarai
Wani malami ya bayyana da wata Fatawa data dauki hankulan mutane wadda ba'a saba jin irin ta ba. Yace idan mutum na Azumi ya yi niyyar tarawa da iyalinsa, ko da bai aikata ba, Azuminsa ya karye. Da yawa dai sun bayyana cewa basu san da wannan aabon keratun nasa ba. https://www.tiktok.com/@muhammadsunnahaljosawy/video/7607127839242079506?_r=1&_t=ZS-93yIreDk7ov
Da Duminsa: Gwamnatin tarayya ta shigar da Malam Nasiru Ahmad El-Rufai kara kotu

Da Duminsa: Gwamnatin tarayya ta shigar da Malam Nasiru Ahmad El-Rufai kara kotu

Duk Labarai
Rahotanni sun tabbatar da cewa, Gwamnatin tarayya ta shigar da malam Nasiru Ahmad El-Rufai kara kotu. Gwamnatin ta shigar da Malam Nasiru Ahmad El-Rufai kotu ne bisa zargin maganar da yayi ta cewa yana sauraren duk wayar da me baiwa shugaban kasa shawara kan harkar tsaro, Malam Nuhu Ribadu ke yi. Malam Nasiru Ahmad El-Rufai ya bayyana hakane a wata hira da aka yi dashi a Arise TV. Shahararren lauya, Deji Adeyanju ne ya wallafa takardar shigar da karar a shafinsa na X. https://twitter.com/i/status/2023345858058821654 https://twitter.com/i/status/2023345858058821654
Ciki da gaskiya :Kalli Yanda Malam Nasiru Ahmad El-Rufai ya cika mota Hilux da takardu dake dauke da bayanan yadda ya kashe duka kudaden da ya samu lokacin yana Gwamnan Kaduna

Ciki da gaskiya :Kalli Yanda Malam Nasiru Ahmad El-Rufai ya cika mota Hilux da takardu dake dauke da bayanan yadda ya kashe duka kudaden da ya samu lokacin yana Gwamnan Kaduna

Duk Labarai
Malam Nasiru Ahmad El-Rufai ya cika motar Hilux da takardu dake dauke da bayanan yanda ya samu kudi da yanda ya kashesu lokacin yana Gwamna. Malam ya tafi da motar zuwa ofishin EFCC a yau, Litinin. Daya daga cikin yaransa ne ya bayyana hakan. https://twitter.com/i/status/2023334251996090732 https://twitter.com/i/status/2023328744392274366
Kalli Bidiyon Da Duminsa: An Harbawa magoya bayan Malam Nasiru Ahmad El-Rufai barkonon tsohuwa yayin da suka yi dandazo a ofishin EFCC

Kalli Bidiyon Da Duminsa: An Harbawa magoya bayan Malam Nasiru Ahmad El-Rufai barkonon tsohuwa yayin da suka yi dandazo a ofishin EFCC

Duk Labarai
A yayin da a yau, Tsohon Gwamnan jihar Kaduna, Malam Nasiru Ahmad El-Rufai ke amsa gayyatar da EFCC ke masa ya tafi ofishinsu. Magoya bayansa sun fito suna zanga-zangar nuna goyon baya a gareshi inda suka taru a kofar ofishin EFCC. Saidai an banka musu Barkonon tsohuwa inda aka ga suna ta rufe hancinsu. https://twitter.com/i/status/2023345645709648175
Da Duminsa: Kalli Bidiyon yanda Malam Nasiru Ahmad El-Rufai ya kama hanyar zuwa ofishin EFCC dan amsa gayyatar da suka masa

Da Duminsa: Kalli Bidiyon yanda Malam Nasiru Ahmad El-Rufai ya kama hanyar zuwa ofishin EFCC dan amsa gayyatar da suka masa

Duk Labarai
Malam Nasiru Ahmad El-Rufai ya kama hanyar zuwa ofishin EFCC dan amsa gayyatar da suka masa. An ga dandazon mutane sun taru sun yi masa rakiya. https://twitter.com/i/status/2023328871341498393 Dama dai malam Nasiru Ahmad El-Rufai ya bayyana cewa a ranar Litinin zai amsa gayyatar da EFCC suka masa. https://twitter.com/i/status/2023330883105673619