Saturday, April 25
Shadow
Wannan wasu Kiristoci ne da aka kama sun yiwa wani me gari aika-aika a jihar Filato, da farko dai an zargi Fulanine suka yi ta’asar

Wannan wasu Kiristoci ne da aka kama sun yiwa wani me gari aika-aika a jihar Filato, da farko dai an zargi Fulanine suka yi ta’asar

Duk Labarai
Wannan wasu Kiristoci ne da aka kama sun yiwa me garin Kwallak a jihar Filato aika-aika, suka aikashi ga mahaliccinsa. Da farko dai an yi zargin cewa, Fulanine suka yi wannan ta'asar amma da dubu ta cika an gane Kiristoci ne 'yan garin. Nan take dai matasa suma suka aiwatar musu da irin abinda sukawa me garin. https://twitter.com/i/status/2047954397779407014
Da Duminsa: Jam’iyyar ADC ta bayyana wata Mugunta da APC ta shirya mata

Da Duminsa: Jam’iyyar ADC ta bayyana wata Mugunta da APC ta shirya mata

Duk Labarai
Jam'iyyar ADC tace a taron da take a jihar Oyo, jam'iyyar APC ta shirya mata wata Mugunta. Ta bayyana hakane ta bakin me magana da yawunta, Bolaji Abdullahi inda tace ta bankado muguntar ta APC ta yunkurin hanata taron nata. Saidai ADC tace wannan ba zai hana ta ci gaba da gudanar da ayyukanta ba dan tasan 'yan Najeriya na tare da ita. https://twitter.com/i/status/2047910299613737336
Kalli Bidiyon: Ina da Ilimin Taurari kuma na hango cewa duk matar data karbi Atamfar da Gwamna ke Rabawa sai ta rabu da mijinta>>Inji Kwankwaso

Kalli Bidiyon: Ina da Ilimin Taurari kuma na hango cewa duk matar data karbi Atamfar da Gwamna ke Rabawa sai ta rabu da mijinta>>Inji Kwankwaso

Duk Labarai
Wani Bidiyo tsohon gwamnan Kano, Dr. Rabiu Musa Kwankwaso ya bayyana a kafafen sada zumunta inda aka ji yana cewa yana da ilimin taurari. Kwankwaso ya bayyana cewa, mata wanda ke da niyyar karbar atamfofin da Gwamna ke shirin rabawa su yi hattara Yayi gargadin cewa duk wadda ta karbi Atamfar sai aurenta ya mutu. https://twitter.com/i/status/2047664007952130441
Kalli Bidiyon: Ba zamu yadda mazan mu su zama saidai mu taba musu inda zasu ji dadi ba amma su ba zasu taba mana ba>>Inji Wadanna  matan dake koya yanda ake Sàdùwàr Aure

Kalli Bidiyon: Ba zamu yadda mazan mu su zama saidai mu taba musu inda zasu ji dadi ba amma su ba zasu taba mana ba>>Inji Wadanna matan dake koya yanda ake Sàdùwàr Aure

Duk Labarai
Wasu mata 'yan Arewa dake nuna yanda ake saduwar Aure suna bayar da shawara sun bayyana cewa ba zai yiyu miji saidai kai ne zaka rika taba masa inda zai ji dadi ba amma kai ba zai taba maka ba. Sun ce dolene idan suka tabawa mijinsu inda zai ji dadi shima ya taba musu inda zasu ji dadi Sannan sun ce ba zasu yadda da namiji me saurin kawowa ba. https://twitter.com/i/status/2047702958410801214
Allah Sarki Kalli Bidiyon hirar tsohon dan wasan Arsenal, Emmanuel Eboue wanda ya auri baturiya, saidai yanzu yace ta rabashi da ‘ya’yanshi sannan ta kwace duka kadarorin da ya mallaka

Allah Sarki Kalli Bidiyon hirar tsohon dan wasan Arsenal, Emmanuel Eboue wanda ya auri baturiya, saidai yanzu yace ta rabashi da ‘ya’yanshi sannan ta kwace duka kadarorin da ya mallaka

Duk Labarai
Tsohon dan wasan Arsenal, Emmanuel Eboue ya koka da maganar hanashi mu'amala da 'ya'yansa da matarsa ta yi. Matarsa dai 'yar kasar Belgium ce kuma a lokacin da yake ganiyarsa ya aureta, saboda rashin Ilimi ya mika mata ragamar komai na kudinsa. Saidai ta yi amfani da wannan dama wajan arzuta kanta ta mallakawa kanta duka kadarorinsa har kotu aka shiga amma ita tayi nasara sannan kotu ta bata damar kula da 'ya'yansu. Yace a yanzu ta hanashi ganawa da 'ya'yan nashi kuma yana da lambarsu, zai aika musu da sako amma ba zasu aika masa da amsa ba. https://twitter.com/i/status/2047596617172144593
Ya fita wajan cin abinci da Budurwarsa ta ci abincin Naira Miliyan 1 a zama daya

Ya fita wajan cin abinci da Budurwarsa ta ci abincin Naira Miliyan 1 a zama daya

Duk Labarai
Wani me hada mata da maza masu neman aure ya koka da wata da ya hadata da wani mutum. Yace ya hadata da mutumin ne inda a ranar farko da suka fita taci abincin Naira 200,000. Yace a rana ta biyu da suka fita ta kawo abokanta 4 inda suka ci abincin Naira 1,053,000. Saurayin yace zai biya kaso 70 cikin 100 na kudin su kuma su biya sauran amma suka kiya. Daga baya dai saurayin ya tafi ya barsu sai da aka rike motar daya daga cikinsu a gidan abincin.
Siyasa Mugun wasa:Kalli Bidiyon yanda wasu maza suka Tumurmushe wata mata a wajan taron siyasa a Kano

Siyasa Mugun wasa:Kalli Bidiyon yanda wasu maza suka Tumurmushe wata mata a wajan taron siyasa a Kano

Duk Labarai
Bidiyon wajan wani taron siyasa a Kano inda aka ga wata mata a tsakiyar maza tana tafiya da kyar ya dauki hankula. A Bidiyon wasu sun rika kokarin baiwa matar kariya amma da yake mutane sun yi yawa, haka aka rika kutsawa da ita tsakanin mutane ba dadi. Da yawa dai sun ce siyasa ba ta mata bace. https://twitter.com/i/status/2047605175267799168