Sunday, May 17
Shadow
Da Duminsa: Na samu bayanai masu inganci cewa Gwamnati na shirin shyèkyè Malam Nasiru Ahmad El-Rufai>>Inji Timi Frank

Da Duminsa: Na samu bayanai masu inganci cewa Gwamnati na shirin shyèkyè Malam Nasiru Ahmad El-Rufai>>Inji Timi Frank

Duk Labarai
Tsohon sakataren yada labarai na jam'iyyar APC, Timi Frank ya bayyana cewa, ya samu bayanai masu inganci dake tabbatar da cewa, Gwamnatin tarayya na shirin Shyèkyè malam Malam Nasiru Ahmad El-Rufai. Ya bayyana cewa ya samu bayanan ne daga wata majiya ta tsaro. Inda yayi zargin cewa, za'a sako Malam Nasiru Ahmad El-Rufai amma za'a bashi wani abu wanda bayan an sakeshi ba zai dade ba zai koma ga Allah. Yace a tabbatar da lafiyar malam Nasiru Ahmad El-Rufai kuma duk abinda ya sameshi alhaki akan Gwamnati ne.
Kalli Bidiyon Da Duminsa: Wani ya tsere da kayan zabe a mazabar Farfesa Isa Ali Pantami, ba’a yi zaben fidda Gwani ba

Kalli Bidiyon Da Duminsa: Wani ya tsere da kayan zabe a mazabar Farfesa Isa Ali Pantami, ba’a yi zaben fidda Gwani ba

Duk Labarai
Rahotanni daga Pantami Jihar Gombe na cewa, sakataren jam'iyyar na yankin ne ya tsere da kayan zaben ba'a samu an gudanar da zaben fidda gwani ba a mazabar. Daya daga cikin yaran Farfesa Pantamin ne ya fito kafafen sada zumunta yana bayyana hakan. An ga Bidiyon sa yana cewa basu yi zaben fidda gwani nba, sakataren ne ya tsere da kayan zaben a kan mashin da wani. https://twitter.com/i/status/2055649488316854439
Da Duminsa: Kalli Bidiyon yanda akawa wani babban dan APC na jaki a wajan Zaben fidda gwani

Da Duminsa: Kalli Bidiyon yanda akawa wani babban dan APC na jaki a wajan Zaben fidda gwani

Duk Labarai
Rahotanni sun bayyana cewa, an yiwa shugaban jam'iyyar APC na karamar hukumar Igabi dake jihar Kaduna na jaki a wajan zaben fidda gwani a jihar. An ga yanda mutane ke ta iface-iface a wajan zaben inda aka ga ana ta turmitsutsu. Bidiyon ya dauki hankula a kafafen sada zumunta inda wasu ke cewa hakan ya dace, wasu na cewa bai dace ba. https://twitter.com/i/status/2055594662719607188
Da Duminsa:Na gano wasu na shiryamin Makarkashiyar game da takarar Gwamnan jihar Gombe>>Inji Hon. Sheikh Isa Ali Pantami

Da Duminsa:Na gano wasu na shiryamin Makarkashiyar game da takarar Gwamnan jihar Gombe>>Inji Hon. Sheikh Isa Ali Pantami

Duk Labarai
Tsohon Ministan Sadarwa, Farfesa Isa Ali Pantami ya bayyana cewa, ya gano wani shirin Makarkashiya da ake shirya masa a game da takarar Gwamnan jihar Gombe da ya fito. Ya bayyana cewa, Wasu ne suka yi riguna da fastarsa a jikin rigunan suka saka dan kawo hargitsi a wajan zaben fidda gwani da ake yi a jihar. Yayi kira ga masoyansa da kada su saka irin wannan riga. Yace kuma yana kira ga jami'an tsaro da su dauki mataki akan irin wadannan mutanen. https://twitter.com/i/status/2055573579945607420
Nasan Ba abinda Ahmad Isa, Ordinary Zai iya min, Shiyasa na zhàgèshì kuma babu abinda yamin>>Inji Aminu J. Town

Nasan Ba abinda Ahmad Isa, Ordinary Zai iya min, Shiyasa na zhàgèshì kuma babu abinda yamin>>Inji Aminu J. Town

Duk Labarai
Shahararren me sharhi a kafafen sada zumunta, Aminu J. Town ya bayyana cewa, yasan babu abinda Ordinary President, Ahmad Isa zai iya masa shiyasa ya zageshi. Ya bayyana cewa, kuma da ya zageshin, babu abinda ya faru. Ya bayyana hakane a wani Bidiyo wanda ma'aikacin Brekete family, Hussaini Dan Hajiya ya wallafa yana masa raddi. Dan Hajiya yace ko ba komai Ahmad Isa ya haifi Aminu J. Town, dan haka ya kamata ya girmamashi. https://www.tiktok.com/@hussainidanhajiya/video/7640099657812659476?_r=1&_t=ZS-96PAK2KPkbk
Kalli Bidiyon Yanda ICPC suka hana Iyalan Malam Nasiru Ahmad El-Rufai bashi Abinci

Kalli Bidiyon Yanda ICPC suka hana Iyalan Malam Nasiru Ahmad El-Rufai bashi Abinci

Duk Labarai
Hukumar ICPC ta hana iyalan Tsohon Gwamnan Kaduna, Malam Nasiru Ahmad El-Rufai bashi abinci. Matarsa Aisha ce ta bayyana haka a wani Bidiyo data wallafa a kafafen sada zumunta inda tace gata ta zo kaiwa mijin nata abinci amma ICPC sun hanata ta bashi. Hakanan Dansa, Hon. Bello El-Rufai ya tabbatar da hakan inda yace antinsu ta kaiwa babansu abinci a ofishin ICPC kamar yanda ta saba da yamma amma aka hanata shiga inda aka ce an hana shigar masa da abinci idan yamma ta yi. Hakanan yace Likitansa ma ya je ganinsa aka hanashi ganinsa. Yace wannan take hakki ne wanda bai kamata ba. Ya bayyana cewa suna neman a dawowa da babansu hakkinsa na dan Adam kamar yanda kundin tsarin Mulkin Najeriya ya bashi dama. https://twitter.com/i/status/2055396738496606522
Kalli Bidiyon: Yanda Adam Garba(Raba Gardama) da tsohuwar matar Adam A. Zango, Ameena suke ta taba juna a wani fim ya dauki hankula

Kalli Bidiyon: Yanda Adam Garba(Raba Gardama) da tsohuwar matar Adam A. Zango, Ameena suke ta taba juna a wani fim ya dauki hankula

Duk Labarai
Bidiyon wani sabin Fim da Adam Garba, wanda aka fi sani Raba Gardama da tsohuwar matar Adam A. Zango, Ameena suka fito a ciki ya dauki hankula sosai. Dalili kuwa shine an ga suna yin abubuwan da ba'a aaba gani ba a fina-finan Hausa, watau suna ta taba juna. Wasu dai sun rika tambayar shin An daina tace fim din Hausa ne? Inda wasu ke tambayar ko kuwa a mahaukaciya ta fito a film din. https://www.tiktok.com/@rrproduction2026/video/7639874239390174485?_r=1&_t=ZS-96OEo3S5Tj2
Bidiyon mahajjata daga Jihar Adamawa suna kwana a waje a kasar Saudiyya ya dauki hankula

Bidiyon mahajjata daga Jihar Adamawa suna kwana a waje a kasar Saudiyya ya dauki hankula

Duk Labarai
Mahajjatan jihar Adamawa da suka je kasar Saudiyya sun rasa dakunan kwana inda aka gansu suna kwana a waje. Da yawa da aka yi hira dasu sun bayyana cewa basu da daki kuma suna neman hukumomin jiharsu dana kananan Hukumomin su amma basu gansu ba. An ji wanda ya dauki Bidiyon hana kokawa cewa ya kamata a dauki matakin da ya dace. https://twitter.com/i/status/2054860996850696454