Thursday, April 23
Shadow
Da Duminsa: Da gaskene mun fara karbar Harajin saka Solar a gidaje>>Gwamnati ta tabbatar

Da Duminsa: Da gaskene mun fara karbar Harajin saka Solar a gidaje>>Gwamnati ta tabbatar

Duk Labarai
A jiyane Bidiyo ya yadu sosai bayan da aka ga wani mutum a Legas yana ta fada da jami'an Gwamnati da suka je karbar harajin saka solar da yayi a gidansa. Mutumin dai yace ba zai biya ba. Inda mutane da yawa suka goyi bayansa. Bidiyon ya jawo cece-kuce sosai inda mutane sukai ta bayyana cewa ko da sune ba zasu yadda ba. A martanin Gwamnatin jihar Legas ta bakin me magana da yawun Gwamnan jihar, Wale Ajetunmobi ya bayyana cewa da gaskene akwai harajin sala sola a gida. Yace amma ba ga duka mutanen jihar Legas ba, ana karbar Harajinne kawai a hannun wadanda suke a gidajen Gwamnatin jihar.
Sai da Allah ya min wahayi, kai tsaye yayi magana dani sannan na yadda na karbi shugabancin INEC>>Inji Shugaban INEC Farfesa Joash Amupitan

Sai da Allah ya min wahayi, kai tsaye yayi magana dani sannan na yadda na karbi shugabancin INEC>>Inji Shugaban INEC Farfesa Joash Amupitan

Duk Labarai
Shugaban hukumar zabe me zaman kanta, Farfesa Joash Amupitan ya bayyana cewa, sai da Allah ya masa wahayi kai tsaye kamin ya karbi shugabancin INEC. Ya bayyana hakane a yayin da yake jawabi a wata coci a Abuja. Yace in banda Allah ya bashi tabbacin cewa zai dafa masa kuma zai karfafashi da ba zai karbi shugabancin INEC din ba. Ya kara da cewa, da karfin Allah yasan zai yi nasara a game da komai da yake.
Da Duminsa: DSS sun Gurfanar da Tsohon Gwamnan Kaduna, Malam Nasiru Ahmad El-Rufai kan yiwa wayar me baiwa shugaban kasa shawara akan harkar tsaro, Malam Nuhu Ribadu kutse

Da Duminsa: DSS sun Gurfanar da Tsohon Gwamnan Kaduna, Malam Nasiru Ahmad El-Rufai kan yiwa wayar me baiwa shugaban kasa shawara akan harkar tsaro, Malam Nuhu Ribadu kutse

Duk Labarai
Rahotanni sun bayyana cewa, Hukumar DSS sun gurfanar da tsohon Gwamnan jihar Kaduna Malam Nasiru Ahmad El-Rufai a gaban kotu saboda zargin yiwa wayar me baiwa shugaban kasa, Shawara akan harkar tsaro, Malam Nuhu Ribadu kutse. DSS sun gurfanar da malam Nasiru Ahmad El-Rufai ne bisa zarge-zarge guda 5 inda a baya suke msa zarge-zarge guda 3. Saidai Malam Nasiru Ahmad El-Rufai ya musanta duka zarge-zargen da ake masa. Saidai Lauyan DSS, Oluwole Aladeloye ya nemi a musu shari'a. Saidai Lauyan Malam Nasiru Ahmad El-Rufai, Oluwole Iyamu ya nemi cewa, a dakatar a bashi lokaci ya tattauna da wanda yake wakilta dan ya dade a tsare a hannun jami'an tsaro.
An yi zàngà-zàngàr neman a sauke shugaban INEC a Sokoto

An yi zàngà-zàngàr neman a sauke shugaban INEC a Sokoto

Duk Labarai
Wasu kungiyoyin fafutuka a jihar Sokoto sun yi zanga-zangar neman a sauke shugaban INEC, Farfesa, Joash Amupitan daga mukaminsa. Kungiyoyin sun yi zanga-zangar ne a Ranar Laraba inda suka yi tattako zuwa ofishin INEC. Shugaban zanga-zangar, Yusuf Abubakar ya bayyana cewa, suna neman shugaban kasa, Bola Ahmad Tinubu ya sauke shugaban INEC ko kuma shugaban INEC din ya sauka da kansa.
Farashin dala a kasuwar Chanji a yau, Alhamis

Farashin dala a kasuwar Chanji a yau, Alhamis

Duk Labarai
Farashin dala a kasuwar Chanji ta Gwamnati a yau, Alhamis, 23 ga watan Afrilu 2026 ya kai Naira 1,351.59 NGN akan kowace dala. Hakan na nuna darajar Naira ta yi kasa idan aka kwatanta da farashin da Nairar ta fara dashi a farkon makon da muke ciki na Naira 1,347 NGN akan kowace dala. A kasuwar bayan fage kuwa ta garuruwan Abuja, Legas da Kano, Farashin dalar ya kai Naira 1,465 NGN zuwa Naira 1,480 NGN akan kowace dala.
Kai Duniya: Kalli Bidiyon yanda wani magidanci ya kama matarsa da Qarto a Otal, Matar ta byoshi waje ba kya a jikinta tanata rokonshi yayi haquri

Kai Duniya: Kalli Bidiyon yanda wani magidanci ya kama matarsa da Qarto a Otal, Matar ta byoshi waje ba kya a jikinta tanata rokonshi yayi haquri

Duk Labarai
Wannan Bidiyon wani magidanci ne da ya kamata matarsa na cin amanarsa da wani Qarto a otal. Daya daga cikin ma'aikatan Otal dinne ya sanar da mijin cewa ga matarsa da wani a otal inda ya je ya ganewa idonsa. Saidai ya fito daga Otal din ya shiga mota zai tafi amma matar ta bishi babu kya a jikinta tana rokon ya yafe mata amma yaki. Lamarin dai ya farune a garin Warri na jihar Delta
Daga cikin Sanatoci 106 da ake dasu a majalisar Dattijai, Jam’iyyar APC nada Sanatoci 87>>Inji Akpabio

Daga cikin Sanatoci 106 da ake dasu a majalisar Dattijai, Jam’iyyar APC nada Sanatoci 87>>Inji Akpabio

Duk Labarai
Kakakin majalisar Dattijai, Sanata Godswill Akpabio ya bayyana cewa, cikin sanatoci 106 da ake dasu, guda 87 duk 'yan APC ne. Ya bayyana hakane a wajan zaman majalisar inda yace amma da yawa kamar 20 da wani abu a yanzu haka suna son shiga jam'iyyar ta APC amma ana kan tattaunawa dasu. Yace zai sanar da matsayinsu idan tattaunawar ta kammala. https://twitter.com/i/status/2046979355176231381
Allah Sarki: Kalli Bidiyon yanda iyalan sojojin da ake zargi da yunkurin yiwa shugaba Tinubu Jhuyin mulki ke ta kuka a kotu suna kiran a yiwa mazajensu Afuwa

Allah Sarki: Kalli Bidiyon yanda iyalan sojojin da ake zargi da yunkurin yiwa shugaba Tinubu Jhuyin mulki ke ta kuka a kotu suna kiran a yiwa mazajensu Afuwa

Duk Labarai
A yaune aka gurfanar da sojojin da ake zargin da yunkurin yiwa shugaban kasa, Bola Ahmad Tinubu Jhuyin mulki a gaban babba kotun tarayya dake Abuja. A wajan kotun an ga matan sojojin sun zo suna ta kuka suna rokon a yiwa mazajensu Afuwa. Da yawa sun tausayawa halin da suke ciki. https://twitter.com/i/status/2046975253411176662 https://twitter.com/i/status/2046980133290979501
Kalli Bidiyon Da Duminsa: Gwamnati ta Gurfanar da Sojojin da take zargi da yunkurin yiwa shugaba Tinubu Jhuyin mulki

Kalli Bidiyon Da Duminsa: Gwamnati ta Gurfanar da Sojojin da take zargi da yunkurin yiwa shugaba Tinubu Jhuyin mulki

Duk Labarai
Gwamnatin tarayya ta gurfanar da Sojojin da take zargi da yunkurin yiwa shugaban kasa, Bola Ahmad Tinubu juyin mulki a babbar kotun tarayya dake Abuja. A yaune dai aka fara sauraren karar tasu wadda Gwamnati ta shigar. An ga yanda aka kawo su a motoci bisa rakiyar jami'an tsaro. https://twitter.com/i/status/2046946948045787308
Kalli Bidiyon: Ma’aikata a ma’aikatar kudi sun saka hoton Ministan kudi da shugaba Tinubu ya kora daga aiki, Wale Edun a jikin akwatin gawa yayin da suke murnar sukeshi daga mukamin

Kalli Bidiyon: Ma’aikata a ma’aikatar kudi sun saka hoton Ministan kudi da shugaba Tinubu ya kora daga aiki, Wale Edun a jikin akwatin gawa yayin da suke murnar sukeshi daga mukamin

Duk Labarai
Ma'aikata a ma'aikatar kudi ta tarayya sun saka hoton Ministan kudi, Wale Edun da Shugaban kasa, Bola Ahmad Tinubu ya sallama daga aiki a jikin Gawa suna Murnar sallamarsa daga aiki. An ga yanda ma'aikatan ke bi suna rijistar wai sun je jana'aizarsa. Lamarin ya dauki hankula sosai inda ake ta bayyana mabanbanta ra'ayoyi akai. https://twitter.com/i/status/2046714720854425751