Wednesday, April 29
Shadow
Farashin Dala a kasuwar Chanji a yau, Laraba

Farashin Dala a kasuwar Chanji a yau, Laraba

Duk Labarai
, Farashin dala a kasuwar Chanji ta gwamnati a yau, Laraba 29 ga watan Afrilu na shekarar 2026 na akan Naira ₦1,360 kan kowace dala. Farashin ya dan motsa inda ya kai Naira ₦1,360.19 akan kowace dala, kamin daga baya ya dawo farashin sama. A kasuwar Bayan fage kuwa, farashin na dala ya kamane akan Naira ₦1,400 zuwa Naira ₦1,480 a kasuwannin Abuja, Kano, Lagos, da Fatakwal. Rahotanni sun ce a ranar Litinin data gabata, an sayar da dalar akan Naira 1390 a kasuwar ta bayan fage.
Wannan Bidiyon na shahararriyar me amfani da kafafen sada zumunta ya dauki hankula bayan da aka zargeta da aikawa mijin wata cewa sha’awa ta dameta yayi sauri ya zo wajanta

Wannan Bidiyon na shahararriyar me amfani da kafafen sada zumunta ya dauki hankula bayan da aka zargeta da aikawa mijin wata cewa sha’awa ta dameta yayi sauri ya zo wajanta

Duk Labarai
Kafar x ta cika da cece-kuce da tsokana da zunde bayan da wata shahararriyar me amfani da shafin me sunan @Firdaussyyyy ake zarginta da ta aikawa wani saurayinta wanda yana da mata cewa sha'awa take ji. Lamarin ya bayyana ne a yayin da cece-kuce ya barke tsakaninta da matar mutumin wanda tace ya saketa. Tace ta bar musu shi. Saidai Firdausi ta yi kokarin nuna cewa ba ruwanta da mijin matar Amma matar tace mata tana da sakon da ta aikawa mijin ta cewa tana jin sha'aw ya zo wajanta. Daga nan ne sai fiddausi ta yi shiru. https://twitter.com/i/status/2048835151044485557
Ana bari  Halas dan Kunya: Shiyasa na daina shan Giya>>Inji Tsohon Mataimakin shugaban kasa, Osinbajo

Ana bari Halas dan Kunya: Shiyasa na daina shan Giya>>Inji Tsohon Mataimakin shugaban kasa, Osinbajo

Duk Labarai
Tsohon Mataimakin shugaban kasa, Osinbajo ya bayyana cewa ya daina shan giyane saboda kunya duk da yasan cewa yasan giyar halas ce. Yace dalilin da yasa yake shan giya shine ya gani a baibul cewa Jesus ya mayar da ruwa giya. Yace dalilin da yasa ya daina sha shine, wata rana ya je yayi wa'azi a sansanin majalisar Dinkin Duniya dake Somalia ya kammala sai ya tafi wani gidan cin abinci dan ya sayi giya. Yace yana shiga sai ya tarar da mutane na ta shan giya amma suna ganinsa sai suka boye giyar, yace sai ya matsa kusa da wani yake tambayarsa me yasa suka boye giyar da suke sha? Sai yace ai shi malam ne basa son yaga suna shan giya. Yace daga nan yawa kansa fada yace duk da giyar ba halas bace amma ya daina sha.
Kalli Bidiyon: Yanda Solar Panels da yawa da aka saka a fadar shugaban kasa, an ma dauke janaretan dake fadar saboda yanzu ga Solar

Kalli Bidiyon: Yanda Solar Panels da yawa da aka saka a fadar shugaban kasa, an ma dauke janaretan dake fadar saboda yanzu ga Solar

Duk Labarai
An ga Solar Panels da aka saka a fadar shugaban kasa dake bayar da wutar lantarki ta hasken rana. A Bidiyon an ji wanda suka dauki Bidiyon na cewa, an ma dauke janaretan dake fadar saboda yanzu an saka solar. Shugaba Tinubu dai yace kada a sake zabensa karo na biyu idan bai samar da wutar Lantarki ba. https://twitter.com/i/status/2049132012875722817
Kalli Bidiyon: Ban ce ‘yan Najeriya basu iya Turanci ba, an min muguwar fassara ne, Inji Shugaban Kenya

Kalli Bidiyon: Ban ce ‘yan Najeriya basu iya Turanci ba, an min muguwar fassara ne, Inji Shugaban Kenya

Duk Labarai
Shugaban kasar Kenya, William Ruto ya bayyana cewa, an masa fassara ba daidai bane kan maganar da yayi amma shi bice 'yan Najeriya basu iya Turanci ba. Yace yana kwatance ne cewa duk kasashen Afrika sun iya Turanci amma turancin Najeriya wani lokacin sai an fassara maka sannan zaka gane. https://twitter.com/i/status/2049092464393191544
Kalli Bidiyon: Shugaba Tinubu da Kross irin na Kiristoci a wuyansa, Dino Melaye yace shin wai ko shugaban kasan ya raba kafane, mutana Kirista muna Musulunci?

Kalli Bidiyon: Shugaba Tinubu da Kross irin na Kiristoci a wuyansa, Dino Melaye yace shin wai ko shugaban kasan ya raba kafane, mutana Kirista muna Musulunci?

Duk Labarai
A wani Bidiyo da ya watsu a kafafen sada zumunta, an ga shugaban kasa, Bola Ahmad Tinubu an masa wankan tsarki irin na Kiristoci sannan aka rataya masa Kross. Lamarin ya baiwa mutane mamaki kasancewar kowa yasan Tinubu musulmi ne. Dino Melaye na daga cikin wadanda suka bayyana mamakinsu game da lamarin inda yace shin ko shugaban kasar ya raba kafane? https://twitter.com/i/status/2048893423889813783
Bayan da APC suka ji cewa mina shirin barin ADC mu koma jam’iyyar PRP, har sun samar da wani sabon shugaba na bogi a jam’iyyar ta PRP zasu kawo rikici a cikinta>>Inji ADC

Bayan da APC suka ji cewa mina shirin barin ADC mu koma jam’iyyar PRP, har sun samar da wani sabon shugaba na bogi a jam’iyyar ta PRP zasu kawo rikici a cikinta>>Inji ADC

Duk Labarai
Jam'iyyar ADC ta bayyana cewa, Gwamnatin Shugaban kasa, Bola Ahmad Tinubu ce gwamnati da aka taba yi wadda sam bata da kunya. Jam'iyyar ta bayyana hakane ta bakin me magana da yawunta, Bolaji Abdullahi. Yace wani abin mamaki shine yanda da jin jita-jita cewa 'yan Adawa na jam'iyyar ADC zasu koma Jam'iyyar PRP, har an samu wasu masu ikirarin shugabancin jam'iyyar PRP sun bayyana. Yace Gwamnatin tarayya da APC zasu ci gaba da karyata cewa, basu da hannu a irin wadannan abubuwan amma Duniya tana ganin abinda ke faruwa.