Wednesday, July 8
Shadow
Daya daga cikin yaran Rarara tace zatawa Lukuman tonon Silili

Daya daga cikin yaran Rarara tace zatawa Lukuman tonon Silili

Duk Labarai
Daya daga cikin yaran Rarara me suka Khadija ta yi barazanar cewa zatawa Tauraron fina-finan Hausa, Lukman tonon Silili. Ta bayyana hakane bayan da Lukman ya fice daga tafiyar Rarara ta Triple R inda tace sun sanshi a baya matsiyacine. Ta yi barazanar cewa, idan ya sake fitowa yayi magana akansu, suna da hotuna da shaidar abubuwan da ya rika cewa a tura masa, zata fitar da update dinsa. https://twitter.com/i/status/2074784964625780753
Kalli Bidiyon: Yanda matar tsohon Gwamnan Kaduna, Malam Nasiru Ahmad El-Rufai ke rokon shugaba Tinubu, Kai Uba ne ga kowa dan Allah a sassautawa mijina sharudan beli saboda sharudan da aka saka masa yanzu ba zai iya cika su ba

Kalli Bidiyon: Yanda matar tsohon Gwamnan Kaduna, Malam Nasiru Ahmad El-Rufai ke rokon shugaba Tinubu, Kai Uba ne ga kowa dan Allah a sassautawa mijina sharudan beli saboda sharudan da aka saka masa yanzu ba zai iya cika su ba

Duk Labarai
Matar tsohon gwamnan Kaduna, Hajiya Asiya Nasiru El-Rufai da kishiyarta, Aichatou sun kira taron manema labarai inda a ciki suka roki shugaban kasa, Bola Ahmad Tinubu ya taimaka ya saka baki a maganar shari'ar mijinsu. Tace babu lungu da sakon da bata shiga ba a Kaduna tawa Shugaba Tinubu yakin neman zabe sannan kuma shima mijinta ya masa yakin neman zabe. Tace ba wai sun ce kada a hukunta mijin nasu ba amma a bashi hakkokin da doka tace a bashi na ganin likitansa da bayar da belinsa. Tace suna neman a sassauta sharudan belin da aka gindaya masa inda tace wanda aka saka masa yanzu sun yi tsauri ba zai iya cikasu ba. https://twitter.com/i/status/2074740477606129851