Najeriya ta lallasa kasar Guinea a wasan da suka buga yau da ci 1-0 a ci gaba da gasar neman daukar kofin Nations Cup da ake bugawa a kasar Egypt.
Kenneth Omeruo ne ya ciwa Najeriya kwallonta a yayin da ake mintuna 73 da wasa.
Najeriya dai ta kasance kasa ta farko data tsallake zuwa mataki na gaba a gasar inda kasashe 16 zasu buga wasan neman kaiwa matakin kusa dana kusa dana karshe.
Zaka so karanta 'Yan kwallon Najeriya sun yi fushi da kin biyansu hakkinsu
No comments:
Post a Comment