Shugaban kasa Muhammadu Buhari ya jinjinawa milyoyin ‘yan Nijeriya wadanda suka kau da kai daga kiraye-kirayen da aka rika yi a shafukan sada zumunta akan su fito zanga-zangar juyin juya hali, amma suka ki fitowa suka ci gaba da harkokinsu.
Malam Garba Shehu, Kakakin shugaban kasar shi ne ya bayyana hakan a ranar Litinin a wata sanarwa da ya fitar a birnin tarayya Abuja. Ya ce shugaban kasar ya ji dadin goyon bayan da aka baiwa tafiyar dimokradiyya a Nijeriya.
Ya ce duk da akwai wadansu daruruwan mutane wadanda a bisa cimma muradin kawukansu ne suka fita wannan zanga-zangar amma ba don manufar kasa ba.
Ku biyomu a shafukanmu na sada zumunta dan samun labarai masu kayatarwa:
A shafin twitter zaku same mu a @hutudole
A shafin Facebook zaku samemu a @hutudolehausa
Danna nan dan sanin yanda zaku tallata hajarku a shafin hutudole
No comments:
Post a Comment