Pages

Sunday 26 January 2020

Mafi yawancin 'yan Najeriya Basu Amfana da Tsarin mu ba>>Mataimakin shugaban kasa, Osinbajo

Mataimakin shugaban kasa, Farfesa Yemi Osinbajo ya bayyana cewa duk da kokarin gwamnati na ganin ta tallafawa al'ummar kasarnan, har yanzu mafi yawancin 'yan Najeriya basu amfana da tsarin na tallafin jama'a ba.



Osinbajo ya bayyana hakane a lokacin da yake magana Ranar Asabar a jihar Legas wajan wani shirin Airtel na tallafawa Al'umma inda yace yana yabawa kamfanin na Airtel da wannan bajinta da yayi.

Yace irin wannan kokari na kamfanonine zai cike gibin da gwamnati ta bari wajan tallafin da take baiwa Al-umma.

Ya bayyana cewa gwamnatinsu tana ciyar da yara Miliyan 9.5 a makarantu a jihohi 34 na kasarnan sannan kuma akwai tallagin kudi da ake baiwa wasu mutane kusa  Miliyan a fadin kasarnan.

Ya kara da cewa akwai kuma matasa Dubu 500 da aka dauka aikin N-Power. Saidai yace duk da haka akwai 'yan Najeriya da dama da basu amfana da wannan tsare-tsaren na gwamnatin ba dan haka suke bukatar karin himma wanda kuma sai sun zuba kudade masu yawa.




Ku biyomu a shafukanmu na sada zumunta dan samun labarai masu kayatarwa:

A shafin twitter zaku same mu a @hutudole

A shafin Facebook zaku samemu a @hutudolehausa

Danna nan dan sanin yanda zaku tallata hajarku a shafin hutudole

No comments:

Post a Comment