Pages

Friday 14 February 2020

Hedimasta Ya Yi Wa Daliba 'Yar Shekara Goma Fyade A Cikin Aji

Wani hedimasta na makarantar firamare ta Alhazawa dake karamar hukumar Danja a jihar Katsina, mai suna Kabiru Husaini yana ci gaba da zama a gidan kaso biyo bayan zarginsa da yi wa yarinya daliba 'yar shekara goma fyade.


Hedimastan, wanda mazaunin Sabon Gari ne dake garin Zaria, rahotanni sun nuna cewa ya jima yana amfani da yarinyar a cikin ajujuwan makarantar.

Mahaifin yarinyar, shi ya gano hakan a ranar 26 ga watan Janairu, 2020.

Hedimastan dai zai ci gaba da zama a gidan kaso har zuwa ranar 14 ga watan Afrilu, 2020 kafin gurfanar da shi a gaban kotun majestiri karkashin jagorancin Hajiya Fadile Dikko.







Ku biyomu a shafukanmu na sada zumunta dan samun labarai masu kayatarwa:

A shafin twitter zaku same mu a @hutudole

A shafin Facebook zaku samemu a @hutudolehausa

Danna nan dan sanin yanda zaku tallata hajarku a shafin hutudole

No comments:

Post a Comment