Awanni 74 da gyara wutar lantarki a Birnin Maiduguri dake jihar Borno, Boko Haram ta sake tarwatsa tashar wutar lantarkin garin.
Premium times ta ruwaito cewa, Boko Haram ta dasa Bama-bamai a jikin na’urar wutar Lantarkin wanda daga baya ta tarwatsa su.
Wata Majiyar tsaro ta tabbatarwa da Majiyar hakan. Saida hukumar wutar lantarki ta shafe kusan watanni 2 tana gyara kamin a samu a dawo da wutar Maiduguri.
A baya dai, hutudole.com ya ruwaito muku yanda matasa suka cika titunan Borno suna shewar dawowar wutar.

“It is a major setback for Maiduguri because the tower that was brought down has affected other poles,” he said.
“They planted bombs on each leg of the towér which caused it to go down, and they had also fired at some of the high tension wires that caused the lines to cut into bits,” he added.