Gwamnan jihar Zamfara Bello Matawalle ya bayyana cewa an baiwa ‘yan Bimsigar da suka sace dalibai mata na Jangebe, Talata Mafara Jihar Zamfara Kudi dan kada su sakesu.
Yace kwanansa 4 bai yi bacci ba dan ganin cewa an saki daliban. Saidai be bayyana sunan ko su wanene suka bayar da kudin ba.
Amma yace nan gaba kadan zai fallasa yanda aka sace dalibai matan. Yace masu yiwa zaman lafiyar jihar Zamfara Zagon kasa su kuka da kansu.
“I didn’t sleep for four days. We worked hard for days to ensure the safe return of the girls to their families. We are using kinetic and non-kinetic approaches, and the non-kinetic is working for us. If not, we wouldn’t have successfully negotiated the release of these girls, ” he said. Daily Trust.