Wannan wani Inyamurine daga jihar Imo da Allah ya azurtashi da hasken zuciya ya amshi kalmar shahada jiya Juma'a kamar yanda wani wanda shima musulmin inyamurinne ya wallafa a dandalinshi na sada zumunta da muhawara, shi dai wannan bawan Allah ya zabi sunan Yusuf bayan da ya yi kalmar shada.
ko da a satin daya gabata an samu wata baiwar Allah me suna A'ishat Obi daga dai jihar ta Imo inda ta fito tace ina alfahari da kasancewata musulma , kuma ta karfafawa 'yan uwanta inyamurai gwiwa akan su fito su daina jin tsoron karbar addinin musulunci, kuma su tashi su nemi ilimin addinin.
No comments:
Post a Comment