Wannan wata matashiyace me suna Hauwa Muhammad wadda marainiyace data kammala karatu daga makarantar mata dake Kawo Kaduna inda ta samu sakamako mafi kyau a cikin ajin data fito sannan ta ci zarabawar JAMB da maki 248.
Wata kungiyace me kula da matasan 'yan mata, GCCNigeria ta dauki nauyin karatun Hauwa bayan data daukota tare da wasu sauran 'yan matan 100 daga sansanin 'yan gudun hijira na Maiduguri shekaru 6 da suka gabata.
Hauwa na son karantar Medicine a jami'ar ABU dake Zaria,muna fatan Allah ya cika mata burinta.
No comments:
Post a Comment