Pages

Friday 16 August 2019

Ibrahim Zakzaky ya koma Najeriya

Jagoran 'yan Shi'a a Najeriya Sheikh Ibrahim Zakzaky ya koma gida daga Indiya kwana uku kacal bayan ya je neman magani, yana mai zargin cewa ba a bar shi ya ga likitocinsa ba.


Wani fasinja a jirgin Ethiopian Airlines ya shaida wa BBC cewa tare suka taho da malamin har suka sauka a filin jirgin sama na Abuja.

Shi ma Abdullahi Usman na kungiyar IMN ya shaida wakilin BBC Chris Ewokor cewa shugaban nasu ya iso Abuja daga birnin Delhi ta Addis Ababa da misalin 12 na rana, amma jami'an tsaro sun fice da shi ba tare da barin 'yan jarida sun ganshi ba.

Sai dai gwamnatin Najeriya ta ce "mummunar halayyar da ya rinka nunawa tare kokarin neman mafaka ne" ya sa aka mayar da shi gida.

Wakilin BBC Ibrahim Isa, wanda ya halarci filin jirgin saman, shi ma bai samu ganin malamin ba.







Ku biyomu a shafukanmu na sada zumunta dan samun labarai masu kayatarwa:

A shafin twitter zaku same mu a @hutudole

A shafin Facebook zaku samemu a @hutudolehausa

Danna nan dan sanin yanda zaku tallata hajarku a shafin hutudole

No comments:

Post a Comment