Pages

Wednesday 11 December 2019

Yanda Mamman Daura ya bayar da umarni irin na shugaban kasa ba tare da Sanin Buhari ba>>A'isha Buhari

Uwargidan shugaban kasa, Hajiya A'isha Buhari ta kwarmata cewa akwai wasu Umarnin da dan uwan shugaban kasar, Mamman Daura ke bayarwa ba tare da sanin shugaban kasar ba.



A'isha Buhari a wani sako data aikewa da jaridar Daily Trust ta hannun me magana da yawunta, Sulaiman Haruna tace Mamman Daurane yayi amfani da me magana da yawun shugaban kasa, Garba Shehu wajan fitar da sanarwar rushe ofishin uwargidan shugaban kasa ba tare da sanin shugaban ba.

Ta kara da cewa Garba Shehu da ya kamata ace yana kare kimar shugaban kasa da ta iyalanshi ya mayar da kanshi abin amfanin wasu miutane dan cma burinsu.




Ku biyomu a shafukanmu na sada zumunta dan samun labarai masu kayatarwa:

A shafin twitter zaku same mu a @hutudole

A shafin Facebook zaku samemu a @hutudolehausa

Danna nan dan sanin yanda zaku tallata hajarku a shafin hutudole

No comments:

Post a Comment