Pages

Friday 14 February 2020

Gwamnatin Najeriya ta saka kyautar Miliyan 36 ga duk wanda ya samar da maganin cutar Coronavirus

Ministan Kimiyya da fasaha, Ogbonnaya Onu ya bayyana cewa gwamnatin tarayya na maraba da duk wani gwamnin kimiyyar lafiya da zai samar da rigakafin cutarnan data samo asali daga kasar China watau Coronavirus inda yace duk wanda ya same maganin cutar gwamnati zata karramashi.





Onu ya bayyana hakane Ranar Alhamis inda aka shiryawa wani daraktan ma'aikatar liyafar bankwana bayan Ritayar da yayi.

Yace Najeriya na son shiga gaban kasashen Duniya wajan neman maganin cutar kuma watakila ma maganin nata na cikin dazuzzukan mu, inda yace Najeriya kasace dake da magunguna na gargajiya

Yace akwai tukwicin Naira Miliyan 36 ga duk wanda ya samar da maganin Cutar.



Ku biyomu a shafukanmu na sada zumunta dan samun labarai masu kayatarwa:

A shafin twitter zaku same mu a @hutudole

A shafin Facebook zaku samemu a @hutudolehausa

Danna nan dan sanin yanda zaku tallata hajarku a shafin hutudole

No comments:

Post a Comment