Pages

Tuesday 11 February 2020

Kar ku dogara da gwamnati wajan Neman Aiki>>Gwamnatin tarayya ta gayawa Matasa

Ministan kwadago,Chris Ngige ya jawo hankalin matasa da su dsina tsayawa neman aikin gwamnati me tsoka kawai, su rika yin kokarin fara sana'a ko kasuwanci da zasu dogara da kansu wanda yace anfi samun kudi ta haka fiye da aikin gwamnati.




Ngige ya bayar da misalin cewa a kaf matasan masu kudin Duniya babu wanda ke aikin gwamnati dan haka sana'a da kasuwanci sune suka fi kawo kudi fiye da aikin gwamnati.

Ya bayyana hakane a wani taro da aka gudanara a jihar Edo dan wayar da kan matasa kan neman aikin gwamnati me tsoka wanda jami'in ayyuka na musamman na ma'aikatar kwadago,Martina Nwodu ya wakici ministan.






Ku biyomu a shafukanmu na sada zumunta dan samun labarai masu kayatarwa:

A shafin twitter zaku same mu a @hutudole

A shafin Facebook zaku samemu a @hutudolehausa

Danna nan dan sanin yanda zaku tallata hajarku a shafin hutudole

No comments:

Post a Comment