Pages

Thursday 13 February 2020

Kotun koli ta soke zaben gwamnan Bayelsa na APC

Kotun kolin Najeriya ta soke zaben gwamnan jihar Bayelsa da ke kudu maso kudancin kasar.


Kotun ta soke zaben David Lyon, na jam'iyyar APC mai mulkin kasar ne kwana guda kafin ya sha rantsuwar kama aiki.

Alkalan kotun biyar, wadanda Mai shari'a Mary Odili ta jagoranta wajen yanke hukuncin, sun ce sn soke zaben Mr Lyon ne saboda mataimakinsa Biobarakuma Degi-Eremienyo ya mika wa hukumar zaben kasar takardun bogi domin a bar shi ya tsaya takara a zaben ranar 16 ga watan Nuwambar da ya gabata.

A watan Nuwambar 2019, hukumar zaben kasar INEC ta ayyana Lyon na jam'iyyar APC a matsayin wanda ya lashe zaben gwamnan ranar 16 ga watan Nuwamba, bayan ya samu kuri'u 352,552.

Hakazalika hukumar zaben ta bayyana cewa Mista Douye Diri na jam'iyyar PDP ya samu kuri'u 143,172.







Ku biyomu a shafukanmu na sada zumunta dan samun labarai masu kayatarwa:

A shafin twitter zaku same mu a @hutudole

A shafin Facebook zaku samemu a @hutudolehausa

Danna nan dan sanin yanda zaku tallata hajarku a shafin hutudole

No comments:

Post a Comment