Pages

Friday 12 April 2024

Sojin ruwan Najeriya sun kama waɗanda ake zargi da satar ɗanyen man fetur

Rundunar sojin ruwan Najeriya ta kama wasu mutane biyu da ake zargin ɓarayin ɗanyen man fetur ne a jihar Bayelsa tare da kama wata babbar mota da kuma wata kirar Mazda ɗauke da lita 1,300 na mai da aka tace ba bisa ka'ida ba.

Wani kwamandan rundunar sojin ruwan ta Najeriya, Commodore Sunday Lakan, yayin da yake gabatar da waɗanda ake zargin a Yenagoa a ranar Alhamis, ya bayyana cewa an samu nasarar cafke mutanen ne bayan samun bayanai na sirri.

"Nan da muka aika jami'anmu zuwa yankin, kuma da isar su ne suka kama motar da ake zargi na ɗauke da ɗanyen mai da aka sace,” inji shi.

Sai dai ya ce lokacin da mutanen suka ga isoar jami'ansu, suka bar suka gudu, inda ya ce sun ɗauki motar zuwa ofishinsu don ci gaba da bincike.

"Don haka, yayin da muke ci gaba da sintiri, mun kama wata mota kirar Mazda 323 ɗauke da ɗanyen mai na sata da dizel da kananzir mai kimanin lita 1,300," in ji Sunday.

Ya kuma ce sun kama wasu mutane biyu mace da namiji waɗanda ke jigilar ɗanyen mai ɗin, inda aka tafi da su domin bincike.

Ku biyomu a shafukanmu na sada zumunta dan samun labarai masu kayatarwa:

A shafin twitter zaku same mu a @hutudole

A shafin Facebook zaku samemu a @hutudolehausa

Danna nan dan sanin yanda zaku tallata hajarku a shafin hutudole

No comments:

Post a Comment