Pages

Tuesday 16 July 2019

ZAN TONA ASIRIN MAGUDIN ZABEN KANO>>KOFA

Rikicin babbar jam'iyyar All Progressive Congress (APC) mai mulki na kara girmama a jihar Kano tsakanin dan majalisa mai wakiltar Kiru da Bebeji, Hon. Abdulmumini Jibrin Kofa da kuma manyan yaran Ganduje irinsu Fa'izu Alfindiki, shugaban jam'iyyar APC na jihar Kano Abdullahi Abbas da sauran su.


Jibrin ya ce matukar wadannan mutane basu sanyawa bakunansu linzami akan irin bakaken maganganun da suke fada a kansa, to babu makawa zai bayyana wani boyayyen asiri na jihar ta Kano.

Haka kuma dan majalisar ya ragargaji shugaban jam'iyyar APC na jihar Kano, Abdullahi Abbas a matsayin mutumin da yake tada zaune tsaye a jihar Kano.
Sarauniya


No comments:

Post a Comment