Pages

Sunday 26 January 2020

Duk wanda cutar lassa ta kashe shahidi ne>>Limami

Limami a masallacin Abdullahi Bin Mas’ud dake unguwar Kabuga ‘yan Azara a jihar Kano, Malam Abubakar Shu’ibu Abubakar, jim kadan bayan idar da sallar juma’a a yau, ya ce, duk musulimin da daya mika al’amuransa ga Allah ya kuma dauki matakan kariya kan annobar cutar zazzabin Lassa.


Ya ce”Duk musulmin da cutar ta Lassa ta hallaka shi to babu makawa ya yi SHAHADA sakamakon ya mutu ne ta sanadiyar cutar”.

Sai dai ya kuma ce “Duk wanda sabo da son shahadar ya ki daukan matakan kariya, ya je ya dauko cutar ta Lassa lahira salama alaikum, to ko kusa bai same shahadar ba, hasalima ya jefa kansane cikin halaka.”


Wakilin mu Ibrahim Abdullahi Sorondinki ya rawaito cewa, limamin masallacin juma’a na Abdullahi Bin Mas’ud dake unguwar Kabuga ‘Yan Azara, Malam Abubakar Shu’aibu Abubakar Dorayi, ya bayyana cewar, cutar zazzabin Lassa da aka samu bullarta a jihar Kano wata jarrabawace da ubangiji ya ke saukarwa al’umma saboda miyagun ayyukan su.
DalaFM




Ku biyomu a shafukanmu na sada zumunta dan samun labarai masu kayatarwa:

A shafin twitter zaku same mu a @hutudole

A shafin Facebook zaku samemu a @hutudolehausa

Danna nan dan sanin yanda zaku tallata hajarku a shafin hutudole

No comments:

Post a Comment