Pages

Friday 14 February 2020

Wani maraya me shekaru 12 ya rataye kansa a Najeriya saboda yana son haduwa da iyayensa a Lahira

Wani maraya mai shekaru 12 ya kashe kansa ta hanyar ratayawa, a kauyen Agboala Ishiala dake karamar hukumar Nkwerre ta jihar Imo a Najeriya.





Yaron mai suna Kasarachi Odurukwe, gabanin mutuwar tasa a ranar Larabar da ta gabata, dan aji 6 ne na wata makarantar firamare da ake kira Practising School.

Ganau daga kauyen dai sun ce, yaron ya rataya kasansa ne da igiyar da ya daure a jikin wata bishiya.

Wani mutumin kauyen da baya so a ambaci sunansa ya ceyaron yana zaune ne a gun kanwar mahaifiyarsa da shi da kannensa, bayan rasuwar iyayen nasu.

Rahotanni na cewa yaron ya sha yin korafi game da yadda rayuwar maraici take, inda yake cewa ya gaji da duniya, saboda haka zai so ya mutu don ya hadu da iyayen nasa da suka mutu; kuma ya sha nanata haka ga sa’o’insa.

Wasu majiyoyi sun ce a gefen rafi ne al’amarin ya auku, bayan ya taya abokansa cike gorunan ruwansu, yaron mai suna Kasarachi ya dauki doguwar sanda ya gwada zurfin ruwan amma bai gamsu ba, daga nan ne ya dauki igiya kamar da wasa, ya rataye kansa, bayan ya yunkura har sau 3, kuma kamar yadda ya bukata, ya ce “ga garinku nan”.

Daga nan ne abokan nasa suka ruga gida suna kururuwa, suka sanar da mummunan al’amarin da ya auku ga manya, inda aka je aka sauke gawar Kasarachi.




Ku biyomu a shafukanmu na sada zumunta dan samun labarai masu kayatarwa:

A shafin twitter zaku same mu a @hutudole

A shafin Facebook zaku samemu a @hutudolehausa

Danna nan dan sanin yanda zaku tallata hajarku a shafin hutudole

No comments:

Post a Comment