Shugaba Buhari ya nada Alkali Tanko Mohammed a watan Junairu bayan dakatar da tsohon Alkalin alkalai, Walter Onnoghen, wanda aka tuhuma da zargin boye kadarorinsa.
An haifi mai Shari'a Tanko a ranar 31 ga Disamba, 1953 a Doguwa, karamar hukumar Giade ta jihar Bauchi.
Ya halarci makarantar gwamnatin Azare inda ya yi karatun sakandare kuma ya kammala a shekarar 1973, sannan ya karasa jami'ar Ahmadu Bello inda ya yi karatun Digir.
Daga baya ya yi karatun Majistir a 1984 da Doktora a jami'ar Ahmadu Bello a shekarar 1998
No comments:
Post a Comment