Pages

Thursday 22 August 2019

Ban San Komai Ba Game Da Ma'aikatar Da Aka Ba Ni Jagoranci, Cewar Sabon Ministan Harkokin Cikin Gida

Sabon ministan harkokin cikin gida na, Ogbeni Rauf Aregbesola ya ce ba shi da masaniya kan yadda harkokin ma'aikatar ke tafiya illa abubuwan da ya ke karantawa daga shafukan jaridu. 


Aregbesola yi wannan jawabin ne yayin da ya ziyarci ma'aikatar jim kadan bayan Shugaba Buhari rantsar da shi kuma ya kuma bashi ma'aikatar da zai jagoranta a ranar Laraba a Abuja. 

Tsohon gwamnan na jihar Osun ya ce, "A gaskiya ban san yadda ake gudanar da ayyuka da tsare-tsare a wannan ma'aikatar ba baya ga abubuwan da na ke karantawa a shafukan jaridu. Ba ni da wata alakar kusanci da ma'aikatar. Abinda na sani shine abinda na ke karantawa a jaridu."

Aregbesola ya umurci Sakatariyar dindindin ta ma'aikatar, Georgina Ehuriah ta cigaba da tafiyar da harkokin har zuwa ranar Litinin kafin ya karbi ragamar jagorancin. 

Ya tabbatarwa dukkan ma'aikatan hukumar da hukumomin da ke karkashinsu cewa zai yi jagoranci na gari inda ya nemi su kara zage damtse domin akwai aiki sosai a gabansu.







Ku biyomu a shafukanmu na sada zumunta dan samun labarai masu kayatarwa:

A shafin twitter zaku same mu a @hutudole

A shafin Facebook zaku samemu a @hutudolehausa

Danna nan dan sanin yanda zaku tallata hajarku a shafin hutudole

No comments:

Post a Comment