Pages

Thursday 22 August 2019

Dangote Ya Ba 'Yan Gudun Hijira A Nijar Gudunmawa Ta Kimanin Dala Dubu 500,000

Treloli goma sha shidda, cike da kayan abinci, da na masarufi wanda a
cewar Gwamnan jihar Maradi Zakari Umaru, ya tashi kimanin million dari
ukku na sefa. Ya kara da cewa, da ma akwai irin su PAM, da HCR, da Gwamnan Sokkoto, da NEMA ta Najeriya dake taimaka musu, kuma an yi musu rijiyoyi sannan ana basu magunguna.


Yanzu haka dai babbar damuwar su, har ma da 'yan gudun hijiran, ingantaccen tsaro ya dawo domin su koma garuruwan su. Wannan shine dalilin da yasa Gwamna Zakari, ya rubuta wa hukumomin yankunan Najeriya wasiku domin su zauna, su samo mafita.

Su ma bayan godiya 'yan gudun hijiran, sun bayanna wa wakiliyar Muryar Amurka Tamar Abari, fatan su na komawa cikin 'yan uwansu, da garuruwansu na ainahi.
VOAhausa.







Ku biyomu a shafukanmu na sada zumunta dan samun labarai masu kayatarwa:

A shafin twitter zaku same mu a @hutudole

A shafin Facebook zaku samemu a @hutudolehausa

Danna nan dan sanin yanda zaku tallata hajarku a shafin hutudole

No comments:

Post a Comment