Pages

Thursday 22 August 2019

Gwamna Zulum Na Jihar Borno Ya Yi Wa Kwamishinonin Sa Iyaka Da Shiga Gidan Gwamnati

A lokacin da ya ke rantsar da Kwamishinonin sa a jiya Laraba, Gwamnan jihar Borno Farfesa Babagana Umara Zulum ya yi wa kwamishinonin sa iyaka da shiga gidan gwamnati, inda ya umurce su da su yi aiki a ofisoshin su wanda mafi yawancin su suke da ofishi a Sakatariyar Musa Usman dake jihar.


Zulum ya ce: "Ku yi aiki a ofisoshin ku dake Ma'aikatar ku na aiki, ba'a gidan gwamnati ba (Government House), sai dai idan gayyatar ku nayi ko kuma wani abun gaggawa daya taso" a cewar sa.

Zulum ya kuma bukaci sabbin Kwamishinonin da suyi aiki tukuru wajen wajen taya shi aiki domin cimma manufin Gwamnatin sa na sake gine jihar Borno.

Gwamna Zulum ya kara bayyana cewa Gwamnatin sa zata ci gaba da kokarin ta don ganin an ciyar da jihar gaba.

A gefe guda kuma Mai Girma Gwamnan ya kirkiri Ma'aikatar Kimiyya da Fasaha da kirkire-kire wanda zai yi aiki don ciyar da jihar gaba ta hanyar kimiyya da fasaha da kuma samarwa matasa ayyukan yi da kuma samarwa jihar kudin shiga.

Zulum ya rantsar da Kwamishinoni guda 19 cikin 22 wanda Majalisa ta tantance su da kuma mashawarta 7 da Mataimakin shugaban ma'aikata a offishin Mataimakin Gwamna, wanda bikin rantsarwa ya gudana a dakin taro na Multipurpose dake Gidan gwamnatin jihar.







Ku biyomu a shafukanmu na sada zumunta dan samun labarai masu kayatarwa:

A shafin twitter zaku same mu a @hutudole

A shafin Facebook zaku samemu a @hutudolehausa

Danna nan dan sanin yanda zaku tallata hajarku a shafin hutudole

No comments:

Post a Comment