Pages

Thursday 22 August 2019

PDP ta soki Buhari kan nadin sabbin ministoci

Yayin da ake ci gaba da tsokaci kan sabbin ministoci 43 da Shugaban Najeriya Muhammadu Buhari ya rantsar a ranar Laraba, PDP ta ce shugaban ya rage masu mukami.


Babbar jam'iyyar adawar ta soki sabon zubin gwamnatin jam'iyyar APC mulki, inda ta bayyana shakku cewa da wuya ta iya kawo karshe matsalolin da Najeriya ke fuskanta da wannan zubin ministocin.

PDP ta bayyana cewa irin mutanen da aka nada ministocin da kuma irin yadda aka raba masu ma'aikatu da za su jagoranta, wata alama ce cewa "da wuya gwamnatin ta iya magance matsalolin da kasar ke fuskanta."




Sakataren jam'iyyar ta PDP na kasa, Sanata Umaru Tsauri, ya ce "kamar Shugaba Buhari bai san matsayinsa ba saboda ya rage wa ministoci mukami kwarai da gaske."

"Shugaban kasa ya ce duk wanda ke bukatar wani abu daga gare shi, to ya bi ta hannun shugaban ma'aikatar fadarsa," in ji Sanata Tsauri.
BBChausa.




Ku biyomu a shafukanmu na sada zumunta dan samun labarai masu kayatarwa:

A shafin twitter zaku same mu a @hutudole

A shafin Facebook zaku samemu a @hutudolehausa

Danna nan dan sanin yanda zaku tallata hajarku a shafin hutudole

No comments:

Post a Comment