Mutanen garin Ibi, mahaifar Wadume sun bayyana cewa labarin kamunshi abin bakin cikine dan kuwa mutum ne me taimako, kamar yanda wani Yahaya me kifi ya bayyana.
"Mutum ne me taimako kuma baya nuna banbancin addini ko kabila", Yahaya ya gayawa Punch.
Maikifi ya ci gaba da cewa"Yanzu haka akwai masallacin da Wadume ke ginawa a garin kuma an kusa kammalashi amma kamun da aka mai zai tsayar da aikin gina masallacin"
"Maganar gaskiya ya taimaki mutane da yawa a garinnan inda wasu ma shine ya zama sanadin arzikinsu sannan rijiyar burtsatsen da yayi mana ba zamu tana mantawa dashi ba" inji Micheal
Saidai tsohon shugaban rukon kwarya na karamar hukumar Ibi, Adasho Johnson ya bayyana cewa sun ji dadin kama Wadume domin kuwa hakan zai sa su samu saukin mamayar da jami'an tsaro suka wa garin nasu suke kama mutane sanadiyyar tserewarshi.
Wani sabon rahoto daga The Nation kuma na cewa a ci gaba da binciken da 'yansanda kewa Wadume ya bayyana musu cewa yana biyan sojojin dake kan hanya dubu 20 dan su barshi ya wuce.
Ya kuma kara da cewa sati 3 da suka gabata ya aika wa da jami'in sojan daya taimaka mishi ya tsere watau Kyaptin Tijjani Balarabe da makudan kudi ta asusun ajiyar kudinshi na banki.
Wata majiyar 'yansanda da ta tsegumtawa The Nation labarin tace a ranar da aka kama Wadume, wasu yaran Kyaftin Balarabe sun kirashi suka gayamai cewa an kama mutuminshi, nan Kyaptin Balarabe ya basu umarnin zuwa su kwatoshi.
Inda bayan sun kwatoshi suka kaishi gidan Kyaptin Balarabe aka kira me walda ya yanke ankwar da aka daura mai a hannu.
Ku biyomu a shafukanmu na sada zumunta dan samun labarai masu kayatarwa:
A shafin twitter zaku same mu a @hutudole
A shafin Facebook zaku samemu a @hutudolehausa
Danna nan dan sanin yanda zaku tallata hajarku a shafin hutudole
No comments:
Post a Comment