Pages

Friday 12 April 2024

Ƙwararrun sojojin Rasha sun isa Nijar don horas da dakarun ƙasar


Ƙwararrun sojin Rasha sun isa jamhuriyar Nijar domin horas da sojojin kasar, a daidai lokacin da Moscow ke ci gaba da ƙarfafa tasirinta a yankin Sahel na yammacin Afirka da ke fama da rikici.

Ƙwararrun sojojin da suka isa Yamai, babban birnin Nijar a ranar Laraba, an gan su suna sauke kaya daga wani jirgin dakon kaya.

“Mun zo nan ne domin horas da sojojin Nijar da kuma bunƙasa haɗin gwiwar sojoji tsakanin Rasha da Nijar,” ɗaya daga cikin ƙwararrun sojin ya shaida wa gidan talabijin na ƙasar RTN.

Masu horas da sojojin za kuma su kawo tsarin tsaro na jirgin sama, a cewar kafar yaɗa labaran.

Isar su Nijar ya zo ne bayan wata yarjejeniyar baya-bayan nan da aka ƙulla tsakanin sojojin Nijar da ke mulki da Rasha domin haɓaka ƙawancen tsaro.

Nijar ta karkata ga Rasha tun bayan da sojoji suka ƙwace mulki a shekarar da ta gabata.

Nijar ta soke daɗaɗɗiyar alaƙar diflomasiyya da tsaro da Faransa kuma kamar Mali da Burkina Faso, tana kusanta kanta ga Rasha domin samun tallafi wajen yaƙar masu iƙirarin jihadi.

Ku biyomu a shafukanmu na sada zumunta dan samun labarai masu kayatarwa:

A shafin twitter zaku same mu a @hutudole

A shafin Facebook zaku samemu a @hutudolehausa

Danna nan dan sanin yanda zaku tallata hajarku a shafin hutudole

No comments:

Post a Comment